Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
Published: 13th, March 2025 GMT
Gidauniyar Attahiru Bafarawa ta fara rabon tallafin kudi naira miliyan goma sha uku da dubu dari takwas ga iyaye mata marayu dari biyu da saba’in da bakwai da masu bukata ta musamman a jihar Sokoto domin tallafawa kananan sana’o’i.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin, Shugaban shirin, Malam Lawal Maidoki ya bayyana cewa, matakin ya yi daidai da kudurin wanda ya kafa na rage radadin tattalin arziki a tsakanin marasa galihu.
Ya bayyana cewa an zabo mutane 12 da suka ci gajiyar tallafin daga kowace karamar hukumar jihar 23 da suka hada da zawarawa 10 ko marayu mata da kuma nakasassu biyu a kowace karamar hukumar.
Ya ce kowane wanda ya ci gajiyar shirin zai karbi naira dubu hamsin tare da tallafin sufurin daga naira 3,000 zuwa naira 5,000, ya danganta da nisan su da wuraren rabon kayayyakin.
Maidoki ya jaddada cewa shirin na da nufin wadata wadanda suka samu tallafin jarin da ake bukata domin biyan bukatunsu na yau da kullum da kuma samar da kudaden shiga, da karfafa tattalin arzikin kasa.
Da yake jawabi a wajen taron, Sarkin Malaman Sokoto, Malam Yahaya Boyi, ya yabawa tsohon Gwamna, Alhaji Attahiru Bafarawa bisa wannan karamci da ya nuna.
Ya mika godiyar wadanda suka amfana, sannan ya bukace su da su yi addu’a ga masu hannu da shuni, Jihar Sakkwato, da Nijeriya, musamman a wannan wata na Ramadan mai albarka.
Boyi ya kuma ja hankalin wadanda suka karba da su yi amfani da kudaden da suka dace ta hanyar yin sana’o’i masu inganci maimakon yin bara.
Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin, Shehu Gwiwa, ya bayyana godiya a madadin sauran jama’a, inda ya gode wa wannan gidauniya bisa tallafin da ta bayar, ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa duk masu hannu a wannan shirin.
Nasir Malali
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bafarawa Rabo Sakkwato wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
A ranar Juma’a da daddare, wata fashewar bama-bama a wata shahararriyar kasuwa a titin Kodesoh, Ikeja dake Lagos ta janyo raunuka ga mutane da dama. Shaidu sun bayyana cewa fashewar ta faru ne lokacin da wani mai kula da shagon kyamara ya yi kokarin bude wani kunshin da aka kawo.
Hukumar agajin gaggawa, tare da jami’an ‘yansanda daga tashar yankin G, EOD-CBRN Base 23 ta Ikeja, da ma’aikatan hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa na jihar Lagos (LASTMA), sun tura jami’ansu domin gudanar da ayyukan daukar matakai da tsaro a wurin.
Kwalara Ta Kashe Mutane 5 A Lagos, An Kai 60 Asibiti Ranga-Ranga Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A YauWani shaida gani da ido, Lucky Okoro, ya bayyana yadda ya samu damar gudu wa daga wurin fashewar, yana mai cewa, “kawai nayi ƙoƙarin shiga shagon, sai fashewar ta afku. Ban jima ba, sai na ga wutar tana kona wani mutum da wata mata a cikin shagon.” Wani shaidar, Olumide Gbeleyi, wanda yake daga wani otel kusa da wurin, ya bayyana cewa, “Mun ji hayaniyar fashewar kuma muka ga hayaki ya rufe ko’ina. Wata mata tana sayar da kayan ciye-ciye a waje ta ji rauni mai tsanani.”
Sule Aminu, wanda ya bayyana yadda abin da ya sani game da lamarin, ya zargi cewa kunshin mai ban mamaki yana dauke da wani abu da aka tura domin cutar da mai shagon.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp