Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai
Published: 13th, March 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, ya tabbatar da cewa ya bar jam’iyyar APC ne da sanin Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.
El-Rufa’i ya bayyana komawarsa jam’iyyar SDP a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a AbujaYa ce bai gamsu da yadda ake tafiyar da APC ba cikin shekaru biyu da suka gabata.
Yayin da yake zantawa da BBC Hausa, El-Rufa’i ya bayyana cewa ya sanar da Buhari kafin ya fice daga APC.
“Na faɗa masa game da shawarar da na yanke a ranar Juma’a. Ina yawan tuntuɓarsa kan harkokin siyasata,” in ji shi.
El-Rufa’i ya kuma tuna cewa lokacin da yake gwamna, ya taɓa miƙa wa Buhari jerin sunayen kwamishinonin da zai naɗa domin ya duba su, don tabbatar da cewa babu wanda ya taɓa zaginsa.
Da aka tambaye shi ko yana da shugabannin siyasa da yake bi, El-Rufa’i ya ce, “Ina da mutanen da nake tuntuɓa kafin na yanke hukunci, kuma Buhari shi ne na farko a cikinsu.”
Game da ko yana nadamar goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sai ya ce, “Ba na nadama, amma wasu abubuwa sun ba ni mamaki.
“Na goyi bayan Tinubu ne saboda wasu shugabannin Musulmi na Yarbawa sun faɗa min cewa an mayar da su saniyar ware a siyasa, kuma na yi imanin cewa dole a bai wa Kudancin Najeriya mulki domin yin adalci da daidaito.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Buhari tsohon gwamna El Rufa i ya
এছাড়াও পড়ুন:
Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
Wata kotu a Amurka ta umurci Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta ƙasar (FBI) da ta fitar da bayanan sirri da aka samu kan Shugaba Bola Tinubu a lokacin wani binciken badaƙalar miyagun ƙwayoyi da gwamnatin ƙasar ta yi a shekarun 1990.
Jaridar Premium Times ta ruwaito Alƙalin kotun, Beryl Howell wanda ya ba da umarnin a ranar Talata, yana mai cewa babu ma’ana a rufe bayanan ba tare da an bayyana wa jama’a ba.
’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasarA watan Yunin 2023 ce wani Ba’Amurke, Aaron Greenspan, a ƙarƙashin dokar ’yancin fitar da bayanai (FOAI) ya miƙa buƙatar a ofishin zartarwa na lauyoyin Amurka, da Hukumar FBI da Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (DEA) da kuma Hukumar Leƙen Asiri ta (CIA).
Wasu bayanai na cewa, a shekarar 1993 ce Tinubu ya sarayar da kimanin Dala 460,000 ga gwamnatin Amurka bayan mahukunta sun alaƙanta kuɗin da fataucin miyagun ƙwayoyi.
Ana iya tun cewa, wannan hujja ta rashin cancantar tsayawa takara manyan ’yan adawar Shugaba Tinubu — Atiku Abubakar da Peter Obi — suka gabatar a yayin ƙorafin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.
Sai dai kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen ta yi watsi da ita tana mai tabbatar da nasarar Tinubu a babban zaɓen ƙasar ma 2023.