Aminiya:
2025-04-14@18:17:16 GMT

Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi

Published: 13th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya tabbatar wa mutanen da hare-haren Lakurawa a ƙaramar hukumar Arewa ya raba da muhallansu cewa gwamnatinsa za ta ɗauki matakan gaggawa domin mayar da su garuruwansu.

Nasir Idris ya bayyana hakan ne lokacin da ya kai ziyarar jaje ga mutanen da hare-hare ya raba da garuruwansu a sananin ƴangudun hijira da ke Kangiwa a jihar ranar Laraba.

Peter Obi na ganawar sirri da gwamnan Bauchi ’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina

Sansanin ya tanadi waɗanda suka rasa muhallansu daga garuruwan Birnin Debe da Dan Marke, da Tambo, ne ke samun mafaka a sansanin inda wasu mahara ɗauke da makamai suka kai hari a ranar Asabar ɗin da ta gabata, inda suka kashe mutum 11 tare da ƙona gida ɗaya daga cikin ƙauyukan.

A wata sanarwa da mai baiwa gwamnan shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Yahaya Sarki ya fitar, ta ce Gwamna Idris ya kai ziyarar ne domin jajanta wa mutanen tare da ganewa idonsa halin da suke ciki, domin sanin matakin da gwamnatinsa za ta ɗauka.

Idris wanda ya bayyana alhininsa kan asarar rayuka da dukiyoyin da aka yi, ya yaba wa jami’an tsaro kan ƙoƙarin da suke yi na shawo kan rikicin.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda ake yawan samun hare-haren daga Jihar Sakkwato da ke maƙwabtaka da Jamhuriyar Nijar.

“Na yaba wa Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa bisa gaggauta kafa sansanin ‘yan gudun hijira kamar yadda na umarce shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Jihar Kebbi Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza

Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan cibiyoyin makamai na HKI wadanda suka Yaffa (tel aviv) saboda daukar fansa kan kashe-kashen da take yi a Gaza.

Tashar talabijin Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran YAF na kasar Yemen yana fadar haka a jiya Jumma’a, ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan unguwar Shaja’iyya inda suka kashe Falasdinawa da dama.

Ya zuwa yanzu tun fara yakin tufanul Aksa, a cikin watan Octoban shekara ta 2023, falasdinawa kimani 51,000 sannan wasu 115,688 a gaza. Ta kuma rusa kimani kasha 90% na gine-ginen Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Bam Ya Hallaka Mutane 8, Wasu da Dama Sun Jikkata A Borno
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno