Yara mata kimanin 74,452 ne suka amfana da tallafin kudi karkashin shirin Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE) a kananan hukumomi 19 na jihar Kano, wanda ya kunshi rukuni na farko da na biyu.

AGILE wani shiri ne na Bankin Duniya tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, wanda aka kirkira don inganta damar samun ilimin sakandare ga yara mata masu shekaru tsakanin 10 zuwa 20.

Shirin yana daukar matakai da dama domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi ga yara mata, ciki har da gina da gyara makarantu, da bayar da tallafin kudi ga iyalai masu karamin karfi, da yakar al’adu da ke hana ‘yan mata zuwa makaranta, da karfafa yara mata  fasahar zamani, da kasuwanci, da kuma dabarun rayuwa.

a ziyarar da tawagar Kano AGILE (Component 2.1) ta kai zuwa wasu makarantun sakandare a karamar hukumar Makoda, wato GGSS Maitsid, da GGSS Koguna da GGSS Sabon Ruwa, wadanda suka amfana da shirin, sun bayyana cewa tallafin kudi na AGILE  ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa iliminsu.

Daliban sun ce sun yi amfani da kudin ne wajen koyon sana’o’in hannu kamar su siyar da kayan kamshi da alewa, da kuma sayen kaya na makaranta kamar uniform, da  takalma, da littattafai, da jakunkunan makaranta.

Sun godewa shirin bisa irin tallafin da suka samu.

A nata jawabin, Mataimakiyar Shugaban Tawagar Component 2.1, Hajiya Abu Umar Muhammad, ta bayyana cewa sun kai ziyara Koguna a Makoda domin gano matsalolin da ‘yan mata ke fuskanta wajen karbar kudin tallafi.

Ta ce wasu suna fuskantar matsala da katin ATM, wasu suna samun matsala da sunayensu, da dai sauran matsaloli.

Ta kara da cewa an shigar da ‘yan mata 74,452 a rukuni na farko da na biyu, yayin da 39,000 suka shiga mataki na uku na shirin.

Shugaban karamar hukumar Makoda, Alhaji Auwal Isah Jibga, ya jaddada cewa shirin ya taimaka sosai wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin karamar hukumar da jihar baki daya.

Ya bukaci a ci gaba da shirin kuma ya shawarci dalibai da su yi amfani da kudin ta hanya mafi dacewa da yadda aka tsara.

Wakiliyar Radio Nigeria ta bayyana cewa kafin hakan, tawagar AGILE Component 2.1 ta kai ziyara karamar hukumar Bebeji, inda suka tattauna da dalibai, da malamai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

Daga Khadija Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

NNPC Da Dangote Na Shirin Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Kan Sayen Ɗanyen Mai

Masana na gargaɗin cewa idan NNPC ta daina sayar wa matatar Dangote mai a naira, hakan na iya haifar da hauhawar farashin man fetur, maimakon rage farashin da ake tsammani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Martani Jagora Ga Trump kan Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Uwargidan Tinubu Ta Bai Wa Mata Manoma Tallafin Naira Miliyan 26 A Nasarawa
  • Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Na Cigaba Da Ba Da Rarar Kudi Ga Alhazan 2023
  • Gwamnatin Bahrain Ta Kara Kaimi Wajen Kama Yan Adawa Daga Ciki Har Da Yara Kanana
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Hukunta Masu Almundahana A Shirin Ciyarwar Azumi
  • Natasha ta yi ƙarar Akpabio a Majalisar Dinkin Duniya
  • NNPC Da Dangote Na Shirin Ƙulla Sabuwar Yarjejeniya Kan Sayen Ɗanyen Mai
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya