Leadership News Hausa:
2025-03-13@20:38:18 GMT

Peter Obi Ya Ziyarci Bauchi, Ya Gana da Gwamna Bala Mohammed

Published: 13th, March 2025 GMT

Peter Obi Ya Ziyarci Bauchi, Ya Gana da Gwamna Bala Mohammed

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour (LP) a 2023 kuma tsohon gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, ya kai ziyara Jihar Bauchi a ranar Alhamis don wata ganawa ta musamman.

Da isarsa filin jirgin sama na Sir Abubakar Tafawa Balewa, Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Rt. Hon. Mohammed Auwal Jatau, ne ya tarɓe shi.

Obi ya ziyarci Gwamna Bala Mohammed a fadar gwamnati, inda suka yi wata ganawar sirri.

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi Gwarzon Ɗan Kasuwa Na Shekarar 2024: Benedict Peters

Duk da cewa dalilin ziyarar bai fito fili ba, ana hasashen cewa yana da alaƙa da shirin siyasar 2027, inda ake ta raɗe-raɗin haɗakar ‘yan adawa domin ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki.

Taron ya ƙara hura wutar jita-jitar haɗakar jam’iyyun adawa, musamman bayan ganawar da Atiku Abubakar ke yi da manyan ‘yan siyasa irin su Obi da kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Hukunta Masu Almundahana A Shirin Ciyarwar Azumi

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta jaddada kudurin ta na tabbatar da gaskiya da adalci a shirin ciyarwa na azumin watan Ramadan da ke gudana a fadin jihar.

Shugaban kwamitin duba rabon abincin buda baki kuma wakilin mazabar Kiyawa, Alhaji Yahaya Muhammad Andaza, ya bada tabbacin haka lokacin da ya kai ziyarar bazata a wasu cibiyoyin ciyarwar.

A yayin ziyarar, kwamitin ya duba yadda ake gudanar da shirin a kananan hukumomin Birniwa da Kirikasamma da Guri da Hadejia, inda aikin kwamatin ya mayar da hankali ga tantance nasarar shirin da gano matsalolin da ke bukatar gyara.

A karshen ziyarar, Alhaji Yahaya Andaza wanda shi ne mataimakin mai tsawatarwa na majalisar, ya bayyana damuwa kan wasu kura-kurai da aka samu a cibiyar bada abincin buda baki ta garin Birniwa ta Farko, inda aka gano wasu matsaloli na rashin bin cikakken tsarin rabon abincin ga masu azumi.

Sai dai kuma, ya yaba da namijin kokarin wasu daga cikin masu dafa abinci a Kirikasamma da Hadejia, da Kasuwar Kofa, da Guri, inda shirin ke tafiya da yadda yakamata.

Wani matashi mai suna Abubakar Idris da ke kula da cibiya ta biyu a garin Guri ya samu kyakkyawan yabo daga ‘yan kwamitin, bisa tsarin da ya bi, inda a cibiyarsa ake samun dafadukar shinkafa mai kyau, hade da kifi da kwai, ko naman kaza, da kuma rarraba  kunu da kosai  a kullum ga masu azumi 300.

A cewar Usman Zakar Ayuba, jami’in kula da cibiyar Hadejia, sama da mutane 8,000 ne ake sa ran za su ci moriyar shirin a kullum a karamar hukumar Hadejia kadai.

Yana mai cewar, an kara cibiyoyi guda biyar a kan guda 22 da ke aiki a mazabu 11 na karamar hukumar.

Kazalika, Shugaban kwamatin Alhaji Yahaya Andaza ya bukaci duk masu dafa abincin azumi na Gwamnatin jihar Jigawan da su kasance masu gaskiya da adalci wajen gudanar da ayyukan su, tare da yin la’akari da darajar watan Ramadan ta hanyar tabbatar da cewa mabukata sun ci moriyar shirin yadda ya kamata.

A don haka, ya gargadi duk masu kokarin yin almundahana da kayayyakin abinci da aka tanada, yana mai cewar duk wanda aka samu da laifi na rage adadin kayan abinci kamar mudu 10 na gero don kunu, da mudu 10 na shinkafa don dafa-duka, da mudu 10 na wake don kosai, zai bandana kudarsa.

Radio Nigeria, ya bamu rahoton cewar, sama da naira miliyan dubu 4 ne gwamnatin Jigawa ta ware domin a ciyar da al’ummar musulmi da ke azumtar watan Ramadan a jihar.

Kwamitin ya kuduri aniyar ci gaba da sa ido a kan duk cibiyoyin ciyarwa a fadin jihar, domin tabbatar da cewar shirin yana tafiya yadda ya kamata.

Majalisar Dokokin ta kuma jaddada aniyarta na hukunta duk wanda aka samu da laifin yin almundahana, tare da daukar matakan da za su inganta shirin.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Inganta Tsaro: Gwamna Nasir Ya Bai Wa Jami’an Tsaro Motocin Sintiri A Kebbi
  • Peter Obi ya yi ganawar sirri da gwamnan Bauchi
  • 2027: Na Shirya Tsaf Don Yin Aiki Tare Da Peter Obi Don Ceto Ƙasar Nan, Gwamnan Bauchi
  • Peter Obi na ganawar sirri da gwamnan Bauchi
  • Boko Haram Sun Yi Yunƙurin Afkawa Tawagar Gwamna Zulum
  • Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
  • HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Sha Alwashin Hukunta Masu Almundahana A Shirin Ciyarwar Azumi
  • Zelensky Ya Ziyarci Saudiyya Don Kawo Ƙarshen Rikicin Ukraine Da Rasha