An Bukaci Jama’a Su Rika Binciken Lafiyarsu Don Kare Kai Daga Cutar Koda
Published: 13th, March 2025 GMT
Babban Rajistara na Sashen kula da lafiyar Koda a Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga, ya yi kira ga jama’a da su kula da lafiyarsu domin kaucewa kamuwa da cututtukan koda.
Ya bayyana hakan ga manema labarai a Gombe yayin bikin Ranar Koda ta Duniya.
Dr. Fidelis Linga ya jaddada cewa wasu munanan dabi’u kamar shan barasa, da taba, da cin abinci mara kyau, da zama babu motsa jiki na daga cikin dalilan da ke haddasa karuwar cututtukan da suka shafi Koda.
Ya yi nuni da mahimmancin yin gwaje-gwaje a asibiti akai-akai, da cin abinci mai kyau, da motsa jiki domin hana cutar koda.
Ya bayyana cewa, a duniya gaba ɗaya, mutane miliyan 850 na fama da cututtukan Koda, kuma daga cikinsu, mutane miliyan 11 ke mutuwa kowace shekara. Ya bayyana wannan matsala a matsayin abin damuwa.
Dr. Fidelis Linga ya ce Asibitin FTH Gombe na kokarin samar da karin na’urorin wanke koda da kuma ƙarin ma’aikatan lafiya domin kula da yawan marasa lafiya da ke zuwa asibitin don wanke Koda.
Ya ce wannan yunƙuri na da nufin inganta samun damar wanke Koda ga marasa lafiya da ke fama da cututtukan koda.
HUDU SHEHU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cutar Koda
এছাড়াও পড়ুন:
An hana tashe bana a Kano — Nalako
Kamar yadda ta riƙa kasancewa a shekarun baya bayan nan, bana ma dai jami’an tsaro sun haramta al’adar nan ta tashe da aka saba gudanarwa daga zarar an kai azumi na goma a watan Ramadana.
Auwalu Sani Nalako, Sarkin Gwagwaren Kano kuma jagoran dabbaka al’adar tashe ne ya tabbatar hakan yayin hirarsa da manema labarai a ranar Litinin.
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da ke Shirin Faruwa A Fagen Siyasar Najeriya ’Yan bindiga sun kashe manoma 14 a OndoNalako ya ce dalilai na tsaro da rundunar ’yan sandan jihar ta bayar ne ya sanya su ma suka dakatar da wasannin tashen na bana.
A cewarsa, jami’an tsaron sun tattaro bayanan sirri da ya tabbatar musu da cewa akwai miyagu waɗanda suke shirin fakewa da tashen domin tayar da hargitsi.
A shekarun baya dai an riƙa samun wasu ɓata-gari da ke ribatar lokacin gudanar da wannan al’ada suna kai hare-hare kan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba.
Al’adar tasheBisa al’ada dai ana yin wasannin tashe ga wanda ya yi aure amma ya mutu, da gidajen masu kuɗi, sarakuna, da sauransu.
Tashe wata al’ada ce da ake gudanarwa daga kwana 10 na watan Ramadan har zuwa daren sallah.
Masu tashe, yawancinsu ƙananan yara, cikin shiga ta ban dariya, sukan zaga kwararo-kwararo a unguwanni da kasuwanni suna nishadantar da mutane da abubuwan barkwanci da ba’a da dai sauransu domin debe musu gajiyar azumi.
Aminiya ta binciko muku asali da tarihi da sauran muhimman abubuwa game da wannan al’ada da ke gudana a cikin watan Ramadan mai alfarma, a kasar Hausa.
Asalin kalmar tasheMasana sun bayyana cewa asalin tashe ana yin sa ne da dare, kuma bakuwar al’ada ce da malam Bahaushe ya samu daga baya.
Farfesa Aliyu Muhammadu Bunza malami ne a Sashen Koyar da Harsunan Najeriya a Jami’ar Usmanu Danfodio da ke Sakkwato.
Ya bayaya wa Aminiya cewa, “Kalmar tashe ta samo asali ne daga a tashi, wato a tashe su daga barci.”
Tarihin tasheIta dai wannan al’ada a cewar Farfesa Bunza, ba a san bahaushe da ita ba sai bayan zuwan Musulunci kasar Hausa.
Tashe “Ya samu tarihin Bahaushe ne a watan azumi na Ramdan; wannan ya nuna bakon abu ne, domin gabanin zuwan Musulunci babu,” inji shi.
Ya ce masana al’ada na ganin tashe ya samo asali ne daga Daular Andalus, “Can ne Musulmi suka kusa kusanta da al’adu, domin da kidin taushi da tashe duk daga can suka samo asali.”
Dalilin yin tasheFarfesa Bunza ya bayyana cewa asalin makasudin yin tashe shi ne a tayar da mutane daga barci su yi sahur a watan azumin Ramadan.
“Har yanzu [a Daular Andalus] suna yin tashen, wanda za a tayar da mutane da dare domin su samu su yi sahur.”
Daga baya “Abin ya koma wasan yara na jan hankalin jama’a da faranta musu rai da debe musu gajiya da takaici da wahala.”
Tashe a al’adar BahausheA ƙasar Hausa akan fara yin tashe ne a 10 na tilas, wato kwana 10 na biyu cikin watan Ramadan domin sanya wa mutane nishadi.
Bahaushe ya kasa watan azumin Ramadan zuwa gida kuna: ‘10 Na Marmari’, ‘10 Na Wuya’, da kuma ‘10 Na Ɗokin Sallah’.
Malamin ya bayyana cewa Bahaushe ya zaɓi ‘10 Na Wuya’ a matsayin lokacin fara tashe.
“A ‘10 Na Marmari Bahaushe ya ga bai ma kamata a yi tashe a lokacin ba, sai an shiga 10 Na Wuya, lokacin an ɗan fara gajiya da azumin.
“Saboda haka sai a riƙa yin tashe ana sa mutane fara’a da farin ciki, su kuma suna ba da kyauta da sadaka.”
Muhimmancin TasheGame da hikima da kuma amfaninsa, Farfes Bunza ya ce tashe kan nuna duk yanayi da mutane suke ciki a shekarar, kuma akwai darasi a cikinsa.
“Su yaran suna kokarin su bayyana halayya da duk wani yanayi da mutane suke ciki.
“Da za a saurari tashen yaran za a ga manyan maganganu ne da manya suka sa musu a baki.
Ya ce, “Cikin tashe ana gina wa yara kunya, kokari, kwazo, son gaskiya, son juna da sauransu.”
Tasirin tashe“Malamai sun gaya mana cewa tashe shi ne musabbabin samuwar wasu fitattun mawakan kasar Hausa; daga wakokin tashe suka samu shahara, maza da mata.
“Saboda haka tashe wani abu ne na sada zumunci da kokarin lurar da mutane [irin] halin da ake ciki, da yadda ya kamata a fuskance su.
“Don yanzu ga shi nan na ga wata yarinya tana tashe a kan bilicin, ba mamaki a samu wata kuma tana tashe a kana ta’addanci.
“Mu nuna wa mutane cewa ta’addanci fa ba zai yiwu ba, dole mu zauna lafiya; saboda haka yaran nan karatu ne suke mana mai zurfi.”