Aminiya:
2025-04-14@16:36:46 GMT

Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu – Obasanjo

Published: 13th, March 2025 GMT

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce galibin ’yan Najeriya suna sha’awar yin amfani da muƙaman gwamnati ne kawai don arzuta kansu da abokan hulɗarsu su durƙusar da ƙasar fiye da yadda suka same ta.

Tsohon Shugaban ƙasar ya ce waɗannan mutane suna karɓar rancen biliyoyin Nairori, suna ganin cewa biyan kuɗaɗen gwamnati bayan an zaɓe su ba zai zama matsala ba.

Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi Peter Obi na ganawar sirri da gwamnan Bauchi

Obasanjo ya bayyana hakan ne a cikin sabon littafinsa mai suna ‘Nigeria: Past and Future’ inda ya zayyana halayen manyan shugabanni a matakin tarayya da na jihohi.

Littafin na ɗaya daga cikin sabbin littattafai guda biyu da aka ƙaddamar domin murnar cikar Obasanjo shekara 88 a makon jiya.

Tsohon Shugaban ƙasar ya ce akasarin waɗanda aka bai wa damar riƙe muƙaman shugabanci a ƙasar nan kamar Gwamnoni, shugabannin ƙasa, Ministoci, Kwamishinoni da shugabannin Ƙananan hukumomi, wasu nada mummunan shiri na son kai, kuma suna da yi niyyar azurta kansu ne yayin da al’ummar ƙasar ke ci gaba da durƙushewa cikin matsanancin talauci da rashin ci gaba.

Obasanjo ya ce, da yawa daga cikin waɗannan suna son zama gwamnoni ko kuma su jagoranci ƙasar nan ta wata hanya ko kuma wasu suna sha’awar yin amfani da ofisoshinsu ne kawai su arzuta kansu da abokan hulɗarsu sannan su bar ƙasar nan fiye da yadda suka same ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yanzu haka al’ummar Borno na cikin zullumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin ƙungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar.

Waɗannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da iƙirarin hwamnati cewa an yi nasarar nakasa ƙungiyar.

Ko mene ne dalilin sake farfaɗowar ƙungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci?

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Wannan ne batun shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16971864-dalilan-farfa-owar-boko-haram-a-jihar-borno.mp3?download=true

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Tsohon Kocin Super Eagles, Christian Chukwu, Ya Rasu Yana Da Shekaru 74
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu