2027: Na Shirya Tsaf Don Yin Aiki Tare Da Peter Obi Don Ceto Ƙasar Nan, Gwamnan Bauchi
Published: 13th, March 2025 GMT
Ya ce, muddin ‘yan siyasan Nijeriya ba su haɗa kansu waje guda ba, ƙalubalen da suke cikin ƙasar nan za su yi wuyar kawuwa. Ya ce, akwai kuma buƙatar tunƙarar matsalolin taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya.
Ya ce, tuntuɓar da suka fara da gwamnan Bauchi a matsayinsa na fitaccen ɗan siyasa a Arewa kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP ya yi ne ba wai don son zuciyarsu ba, illa sai don son da suke yi da cigaban ƙasar nan da nemi mafita.
Ya lura kan cewa akwai buƙatar a fara magance matsalolin talauci a Nijeriya kafin a tunƙari sauran matsaloli. Ya yi fatan cewa za su ci gaba da irin wannan tattaunawar domin nema wa Nijeriya mafita.
Shi kuma a jawabinsa, gwamna Bala Muhammad ya ce, tabbas akwai buƙatar ‘yan siyasa su ajiye ra’ayoyinsu su nemi yadda za su haɗa kai waje guda domin ceto Nijeriya da tabbatar da shugabanci na kwarai, sai ya ce a shirye yake ya yi aiki tare da Peter Obi.
Bala wanda ya misalta Peter Obi a matsayin jagoran ‘yan adawa a Nijeriya, “Ko ma dai menene za a ce, a shirye nake na yi aiki tare da Peter Obi, mun jingine wane wane wane wane domin nemi shugabanci na kwarai a ƙasar nan.”
Bala Mohammed ya ce lokaci ya yi da za a ajiye banbance-banbance a tunƙari haƙiƙanin zahiri tare da kawar da matsalolin da suke damun Nijeriya. Ya kuma ce, ba magana ce ake ta jam’iyya ba, illa sai don ƙasar baki daya.
Daga cikin tawagar Peter Obi akwai tsohuwar ministan kuɗi, Mrs. Nenadi Usman wadanda suka ziyarci Sarkin Bauchi Rilwanu Sulaiman Adamu bayan da suka ziyarci gwamnan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Wajen Inganta Noma, Sufuri Da Ma’adanai
Sanarwar ta ƙara da cewa, tawagar ta Zamfara ta yi hulɗa da kamfanonin Zhong Zhao International Group, Phoenix Wings, Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, da Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd yayin da suke ƙasar Sin.
Tang Zhangwei, ya jagoranci wasu kamfanoni zuwa jihar Zamfara, domin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu a sassa masu muhimmanci, domin bunƙasa tattalin arziki.
A nasa jawabin, gwamna Lawal ya yaba da ƙoƙarin da kamfanonin ƙasar Sin ke yi na tabbatar da nasarar haɗin gwiwarsu.
“Ina so in yi muku barka da zuwa Jihar Zamfara. Muna maraba da ku. A watan Fabrairu, na jagoranci wata tawaga zuwa ƙasar Sin don ganawa da kamfanoni a sassa daban-daban da kuma gano ci gaban da za su samar. Tafiya ce mai tasirin gaske.
“Mun yi haɗin gwiwa da kamfanin ƙasa da ƙasa na Zhong Zhao, wanda ya kware a fannin takin zamani da noman zamani. Suna mai da hankali kan samar da takin gargajiya da fasahar kiwo na R&D. Mun rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna domin horar da manoman gida sana’o’in noma, ta hanyar amfani da injina da fasahar zamani wajen kafa masana’antar takin zamani a jihar Zamfara.
“Tawagar Zamfara ta yi hafin gwiwa da kamfanin Phoenix Wings, wani kamfanin ƙasar Sin da ya ƙware kan fasahar sa ido kan tsaro, gami da jirage marasa matuƙa. A tare, za su bullo da dabarun samar da ingantattun tsare-tsare na magance matsalar ‘yan bindiga, garkuwa da mutane, da ƙalubalen tsaro a jihar Zamfara.
“A taronmu da kamfanin Shenzhen HighGreat Innovation Technology Development Co., Ltd, mun tattauna batun ƙirƙire-ƙirƙire, samar da jirage marasa matuƙa da sauran fasahohi.
“Mun ɗauki nauyin kamfanonin Xiamen Magnetic North Technology Co., Ltd. da Xiamen King Long United Automobile Industry Co., Ltd. An gabatar da shawarwari don bunƙasa cibiyoyin sufuri na zamani da gabatar da tsarin zirga-zirgar jama’a don inganta sufuri a ciki da wajen jihar.
“Bugu da ƙari, mun yi taro mai nasara tare da kamfanin WEICAI LOVOL International Trading Company, wanda ke mai da hankali kan noman zamani, wanda a Turance ake kira ‘Smart Agriculture, ‘Integrated Management Platform’, da amfanin da injinan noma.
“Tawagar Zamfara ta gana da kamfanin Tibet Ming inda suka tattauna batun ƙara zuba jari a harkar haƙar ma’adanai, da jaddada ayyuka masu ɗorewa, ɗawainiyar jama’a, da fasahar zamani don bunƙasa haƙo ma’adinai a jihar Zamfara,” Inji Gwamna Lawal.
Tun da farko, sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, wanda ke cikin tawagar jihar a ƙasar Sin, ya bayyana nasarorin da suka samu a ziyarar aiki.
Ya ce, “Mun kai ziyarar aiki mai inganci a ƙasar Sin, kuma sakamakon ya bayyana a yau bayan da wasu manyan kamfanoni suka zo jihar Zamfara.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp