Shugaba Vladimr Putin Na Kasar Rasha Ya Amince Da Tsagaita Wuta A Yakin Ukraine
Published: 13th, March 2025 GMT
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya bada sanarwan amincewa da tsagaita budewa juna wuta tsakanin Rasha da Ukraine na tsawon kwanaki 30, wanda shugaban kasar Amurka Donal Trump ya gabatar, sai dai akwai bukatar karin bayani filla-filla kan yadda hakan zai kasance. Sannan yana fadar wannan zai kai ga tsagaita budewa juna wata na din din din.
Shafin yanar Gizo na labarai Africa News ya nakalto shugaban yana fadar haka a yau Alhamis. Ya kuma kara da cewa akwai bukatar a kara tattaunawa da abokammu na kasar Amurka don kara fayyace yadda tsagaita wutan zai kasance.
Daga cikin abubuwan da za’a tattauna akwai yiyuwar sabawa yarjeniyar da kuma matakan da za’a dauka don hana hakan faruwa ko kuma idan ya faru matakan da yakamata a dauka, wa kuma zai kula da wannan bangaren.
Sannan ya kara da cewa shin kasar Ukraine zata yi amfani da wadannan kwanaki 30 don ta kara tara makamai da kuma shirin fara sabon yakin ne.
Shugaba Putin ya kara da cewa: Ya amince da tsaida yaki, da kuma fatan tsaida shi zai share hanyar samar da zaman lafiya na din din din tsakanin kasashen biyu da kuma yankin, tare da magance matsalolin da suka haddasa yakin.
Daga karshe shugaban ya godewa shugaban kasar Amurka Donal Trump saboda bada lokacinsa don kashe wutan da ke ci a kasar Ukraine fiye da shekari 3 da suka gabata.
Sannan yace kasar Rasha ba zata amince da sojojin tabbatar da zaman lafiya daga kasahsen kungiyar tsaro ta nato ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Makiya suna cike da takaici da fushi kan ci gaban da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take samu
A yayin ganawarsa da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran a yau Lahadi, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa; Ci gaban da Iran ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu mugun nufi kan lasar ta Iran. Yana mai bayyana cewa, tabbas akwai rauni a fannonin da suka shafi tattalin arziki da ya kamata a magance.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya yi la’akari da cewa; Sojojin kasar suna matsayin kariya ta al’umma da kuma mafakar al’umma daga duk wani mai wuce gona da iri, sannan kuma ya jaddada wajibcin ci gaba da bunkasa shirye-shirye da kayan aiki da tsare-tsare don sauke wannan nauyi na kasa. Ya kara da cewa: Ci gaban da kasar ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu adawa da Iran, kuma ko shakka babu akwai raunin da ya faru a fannonin da suka shafi tattalin arziki da babu shakka akwai bukatar a magance shi. Jagoran ya bayyana shirye-shiryen kayan aikin sojojin a matsayin ma’ana inganta karfin makamansu da inganta tsarin su da kuma yadda suke rayuwa. Ya kara da cewa, “Bugu da ƙari, shirye-shiryen kayan aiki, shirye-shirye ne na gudanar da tsare-tsare – wato imani da manufa da sako da kuma tabbatar da halaccin hanyar – wadanda suke da matukar muhimmanci, kuma akwai ƙoƙari na makiya na neman murguda su.”