HausaTv:
2025-04-14@16:27:26 GMT

Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan

Published: 13th, March 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hamas ta yi gargadi akan cewa; Wata sabuwar yunwa za ta  bulla a Gaza saboda yadda HKI take ci gaba da killace yankin da hana shigar da kayan agaji hatta a cikin watan Ramadan.

Kakakin kungiyar ta Hamas Abdullatif al-Qa’uni wanda ya fitar da wani bayani ya ce; Falasdinawa a yankin Gaza an killace su, makonni biyu a jere, kuma sojojin mamaya sun hana a shigar da kayan abinci,magunguna, da makamashi, wanda hakan yake a matsayin amfani da yunwa a matsayin makamin.

Qa’ani ya kara da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne jefa Falasdinawa cikin yunwa. Haka nan kuma ya ce;  A nan gaba kadan kayakin da ake da su na bukatun yau da kullum za su kare a cikin Gaza, wanda hakan zai kara wahalar da mutanen yankin.

Kakakin kungiyar ta Hamas ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi matsin lamba akan HKI domin bude iyakoki da bayar da damar shigar da kayan agaji.

Tun a farkon wannann watan Maris da muke ciki ne HKI ‘yan mamayar su ka hana shigar da muhimman kayakin da ake bukata zuwa cikin yankin na Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya

Fursunoni a gidajen yarin daban-daban a sassan Najeriya sun koka game da munin irin abincin da ake ba su, wanda suka ce na karnuka ya fi shi.

Da dama daga cikin fursunonin da muka zanta da su sun bayyana cewa takwarorinsu sun sha mutuwa a sakamakon yunwa.

Wannan zargi na zuwa ne bayan da Hukumar Gidajen Yari ta Najeriya tare da wani kwamitin bincike mai zaman kansa sun ƙaryata zarge-zargen fursunonin kan yunwa a gidajen yari.

A watan Satumban 2024 ne Ministan Harkokin Cikin Gida,  Olubunmi Tunji-Ojo, ya kafa a kwamitin domin gudanar da bincike kan zargin jami’an gidajen yari da cin hanci da kuma cin zarafin fursunonin.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

Duk da cewa kwamitin ya tabbatar da zargin yunwa da fursunonin suka yi, Muƙaddashin Shugaban Hukumar Gidajen Yari ta Kasa, ya ce an zuzuta lamarin, saboda a cewarsa, babu alƙaluman da ke tabbatar da hakan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan