Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan
Published: 13th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hamas ta yi gargadi akan cewa; Wata sabuwar yunwa za ta bulla a Gaza saboda yadda HKI take ci gaba da killace yankin da hana shigar da kayan agaji hatta a cikin watan Ramadan.
Kakakin kungiyar ta Hamas Abdullatif al-Qa’uni wanda ya fitar da wani bayani ya ce; Falasdinawa a yankin Gaza an killace su, makonni biyu a jere, kuma sojojin mamaya sun hana a shigar da kayan abinci,magunguna, da makamashi, wanda hakan yake a matsayin amfani da yunwa a matsayin makamin.
Qa’ani ya kara da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne jefa Falasdinawa cikin yunwa. Haka nan kuma ya ce; A nan gaba kadan kayakin da ake da su na bukatun yau da kullum za su kare a cikin Gaza, wanda hakan zai kara wahalar da mutanen yankin.
Kakakin kungiyar ta Hamas ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi matsin lamba akan HKI domin bude iyakoki da bayar da damar shigar da kayan agaji.
Tun a farkon wannann watan Maris da muke ciki ne HKI ‘yan mamayar su ka hana shigar da muhimman kayakin da ake bukata zuwa cikin yankin na Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
Fursunoni a gidajen yarin daban-daban a sassan Najeriya sun koka game da munin irin abincin da ake ba su, wanda suka ce na karnuka ya fi shi.
Da dama daga cikin fursunonin da muka zanta da su sun bayyana cewa takwarorinsu sun sha mutuwa a sakamakon yunwa.
Wannan zargi na zuwa ne bayan da Hukumar Gidajen Yari ta Najeriya tare da wani kwamitin bincike mai zaman kansa sun ƙaryata zarge-zargen fursunonin kan yunwa a gidajen yari.
A watan Satumban 2024 ne Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya kafa a kwamitin domin gudanar da bincike kan zargin jami’an gidajen yari da cin hanci da kuma cin zarafin fursunonin.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoDuk da cewa kwamitin ya tabbatar da zargin yunwa da fursunonin suka yi, Muƙaddashin Shugaban Hukumar Gidajen Yari ta Kasa, ya ce an zuzuta lamarin, saboda a cewarsa, babu alƙaluman da ke tabbatar da hakan.