Aminiya:
2025-04-14@16:46:06 GMT

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai

Published: 14th, March 2025 GMT

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya fasa baragurbin ƙwai kan zargin sace Jafaru Sani, tsohon Kwamishina a gwamnatinsa.

El-Rufai, wanda ya mulki Jihar Kaduna daga 2015 zuwa 2023 kafin ya miƙa mulki ga Sanata Uba Sani, wanda shi ne ɗan takarar da ya fi so ya gaje shi, ya bayyana wannan batu ne a shafinsa na Facebook da aka tantance sahihancinsa a ranar Alhamis.

Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — Obasanjo

A cewarsa, an tsare tsohon Kwamishinan na shi ne a kurkuku ba bisa ƙa’ida ba.

El-Rufai ya ce, yana da tabbacin ana cin zarafin abokin nasa ne saboda ya fice daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.

“An sace abokin aikinmu kuma tsohon kwamishina mai ƙwazo a zamanin mulkin El-Rufai, Malam Jafaru Sani, an sace shi ne a Kaduna da rana tsaka, yana ta hannun ‘yan fashin dajin Uba Sani da ke cewa su ’yan sanda ne!

“An tsare Jafaru a kurkuku ba tare da wata takardar sammaci daga ‘yan sanda ko ta tuhuma daga Ma’aikatar Shari’a ta Jiha ba.

“Bayan bincike, mun gano cewa ana zarginsa da safarar kuɗi. Amma ainihin laifin Jafaru shi ne ficewarsa daga APC zuwa SDP.

“Wannan salon zaluncin iri ɗaya ne da wanda aka taɓa yi wa wani abokinmu, Bashir Saidu, wanda aka sace a ranar 31 ga Disamba, 2024, aka tsare shi na tsawon kwanaki 50 kafin a bayar da belinsa!

“Rawar da wasu alƙalai ke takawa a shari’ar Kaduna abu ne mai matuƙar damuwa. Muna sa ido kuma muna jira domin babu wani yanayi da zai dawwama, kuma ranar hisabi za ta zo.”

Har yanzu gwamnatin Jihar Kaduna ba ta mayar da martani kan waɗannan zarge-zargen da El-Rufai ya yi ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Uba Sani

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan

Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadaccen Abinci, Sanata Abubakar Kayri ne ya bayyana a haka, a cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar.

“Mun samar da tsarin samar da wadataccen abinci a kasar nan, wanda kowanne dan kasar zai amfana da shi”, in ji Kyari.

Daga cikin manyan abubuwan da suka hada da bashin sun hada da; samar da ingantaccen Irin Shinkafa da kuma habaka yadda ake samar da Irin na Shinkafar.

Sauran sun hada da mayar da hankali wajen yin girbin mai kyau, samar da nau’ikan Shinkafar da ke jurewa kowacce irin cutar da ke lalata Irin Shinkafar da aka shuka, aka ajiye a cibiyar gudanar da bincike kan amfanin gona (NCRI) da ke yankin Badeggi a Jihar Neja.

Kazalika, akwai kuma bukatar kara bunkasa kayan aikin gona, inganata aikin malaman gona, amfani da kayan aikin gona na kimiyya domin rika samar da bayanai a kan lokaci, musamman wanda ya shafi sauyin yanayi, samar da farashin kayan amfanin gona a kasuwa, dakile barkewar kwarin da ke lalata amfanin gona da sauransu.

A nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Abdullahi Sabi Abdullahi, ya bayyana gamsuwar da cewa, shuka ingantaccen Irin noma zai taimaka wajen ciyar da daukacin ‘yan Nijeriya gaba.

Dakta Abudullahi ya kara da cewa, ingantancen Iri shi ne, kashin bayan da zai kawo karshen kalubalen da bangeren samar da wadataccen abinci a kasar.

“Wannan hadaka za ta kara karfafawa, musamman kananan manoma na kasar nan guiwa, ta hanyar yin amfani da aikin karfafa wa kanannan manoma gwiwa, wato SHEP, wanda a yanzu aikin ya karade jihohi 14 na kasar nan”, a cewar Abdullahi.

Kazalika, wannan hadakar ta kasance tamkar cike wani gibi ne a tsakanin gudanar da bincike, yin aiki a aikace tare kuma da samar wa manoman kasar nan kayan aikin gona na zamani da kuma samar musu da ilimin kwarewar da ya kamata a fannin na aikin noma.

Shi kuwa, Darakta Janar na Hukumar, wanda kuma shi ne har ila yau, ya jagoranci tawagar kasar ta Japan, Takao Shimokawa ya bayyana cewa, Hukumar ta JICA da kuma Kasar Japan, sun mayar da hankali wajen ganin an bunkasa bangaren noman Shinkafa a Afirka, musamman ma a Nijeriya, duba da cewa, kasar ta kasance kan gaba wajen noman Shinkafa.

Wannan shirin ya nuna a zahiri irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya da Hukumar JICA suka yi, don kara habaka bangaren samar da wadataccen abinci a kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • An Karrama Shugaban Qausain TV, Kanar Sani Bello Da Lambar Yabo
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan