Me Ya Sa Jama’ar Turai Ke Adawa Da Sayen Kayayyaki Kirar Amurka?
Published: 14th, March 2025 GMT
A wani bangare na daban kuwa, dole ne ’yan siyasar Turai su yi tunani cewa, jama’arsu sun dauki irin wannan mataki ne ba ma kawai bisa bukatunsu na sayayya ba, har ma ya kasance mataki ne na nuna adawa da babakeren Amurka, da bukatunsu na dogaro da kansu a bangaren manyan tsare-tsare.
Huldar Amurka da Turai ta wannan fuskar ta yi hannun riga da ainihin ma’anar zumunci, inda lamarin ya yi rauni matuka, kuma tabbas matukar Turai ba ta nemi dogaro da kanta ba, za ta yi asara daga barazana da kalubalen da Amurka take haifarwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci wata tawaga zuwa Jihar Edo domin binciko gaskiyar abin da ya faru game da kisan mafarauta ’yan asalin jihar a ƙauyen Uromi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya umarci a kafa wannan tawaga, wacce ta ƙunshi manyan shugabanni irin su Sarkin Rano, Kwamishinonin ma’aikatu da kuma Shugaban Ƙaramar Hukumar Bunkure.
Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi Yadda Tinubu ya taimaka wa ’yata ta samu aiki a NUPRC — Buba Galadima“Manufarmu a bayyane take – bincike, tattaunawa da bayar da shawarwari masu ɗorewa.
“Wannan ba kawai yawon neman gaskiya ba ne, har ila yau ƙoƙari ne na kawo zaman lafiya, domin hana sake faruwar irin wannan tashin hankali,” in ji mataimakin gwamnan
Tawagar za ta gana da Gwamnan Jihar Edo, hukumomin tsaro, sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin fararen hula domin fahimtar matsalar tare da kawo hanyoyin sasanci.
Gwarzo, ya ce tawagar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an samun zaman lafiya da hana faruwar irin wannan rikici a gaba.
Wannan ƙoƙari na cikin shirin Gwamnonin Arewa na haɗin kai da goyon bayan zaman lafiya a faɗin Najeriya sakamakon ƙaruwar rashin tsaro da ake fuskanta.
“Wannan shiri wani ɓangare ne na matakan haɗin gwiwar Gwamnonin Arewa domin nuna goyon baya, haɗin kai a ƙasa da kuma tunkarar matsalar tsaro da ke ƙaruwa a sassa daban-daban na Najeriya,” in ji shi.