Kwamatin duba Shirin samar da abincin buda baki na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse, ya yaba da kyakkyawan yanayin kosai da kunu da ake samarwa domin rabawa masu azumi a cibiyar bada abincin ta 2 a mazabar Kiyako ta karamar hukumar Birnin Kudu.

Shugaban Kwamatin kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isyaku Abubakar, ya bayyana haka a lokacin rangadin kwamatin.

Ya bayyana bubukatakarin kayan miya wajen dafa shinkafar da ake rabawa masu azumi.

Da ya ke mayar da jawabi, mai samar da abincin buda baki a cibiyar mazabar Kiyako da ke Babaldu, Salisu Sabo, ya ce suna samar da abincin buda baki da ya hada da shinkafa dafa-duka da kunu da kosai, ga masu azumi 300 a kowace rana.

Salisu Sabo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa bullo da tsarin ciyar da masu azumi a fadin jihar.

Kwamatin ya Kai makamanciyar wannan ziyara garuruwan Wurno da Kiyako da kuma Birnin kudu.

Kazalika, ya ja hankalin mai aikin dafa abincin buda Baki a cibiyar Gantsa Yamma ya kara kayan miya da mai wajen dafa shinkafar da ake rabawa jama’a.

Ya yi wannan jan hankali ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin duba Shirin Samar da abincin buda baki a karamar hukumar Buji, inda ya bukaci masu aikin raba abincin su rinka amfani da safar hannu domin tabbatar da tsafta.

Alhaji Sani Isayku Abubakar ya ce kwamatin yana rangadi ne domin tabbatar da ganin cewa masu aikin dafa abincin su na aiki da tsarin gwamnatin jihar Jigawan wajen dafa abincin da rabawa ga jama’a.

Sai dai kuma, ya yabawa mai aikin dafa abincin a Gantsa bakin Tasha bisa gudanar da aikinsa kamar yadda gwamnati ta bada umarni.

Da ya ke mayar da jawabi, mai aikin dafa abincin buda baki a Gantsa bakin Tasha Malam Sani Yusuf, ya ce ana ba su naira dubu 672 duk kwana uku domin dafa shinkafa kwano 10 da kunu na gero kwano 10 da kosai na wake kwano 10.

A nasa bangaren, Jami’in Shirin na karamar hukumar Buji, Malam Tasi’u Ibrahim Gantsa, ya ce an kafa cibiyoyi 20 a fadin karamar hukumar wadda ake bawa naira 672 cikin kwanaki uku domin Samar da shinkafa da kosai da kunu, bisa kudurin gwamnatin jiha na ciyar da jama’a a watan Azumi.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran babban titin Abuja-Kaduna-Zariya-Kano, wadda ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Arewacin Najeriya.

Da yake jawabi a taron kaddamarwar a Kagarko, Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani, ya bayyana yadda aka yi watsi da hanyar da kuma irin mummunan tasirin da hakan ya yi ga rayuka da ci-gaban tattalin arziki.

Gwamna Uba Sani, ya yaba wa Tinubu bisa farfado da aikin, yana mai nuni da muhimmancin hanyar a matsayinta na mafi yawan zirga-zirgar ababen hawa a Arewa.

Da yake ba da tabbacin kamma aikin a cikin watanni 14, Tinubu wanda Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce za a gina titin ne da kankare, kamar babbar hanyar Legas zuwa Kalaba.

An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ministan ya kara da cewa aikin zan dangana har zuwa filin jirgin sama na Kano, kuma za a sanya kyamarorin CCTV gaba daya a tsawon titin, wanda sabon dan kwangila ne zai aiwatar.

Ya ce, shugaban kasa ya amince da naira biliyan 252 don muhimman sassan aikin, inda aka riga aka biya kashi 30%, yanan mai yaba muhimmiyar rawar da Gwamna Uba Sani ya taka a aikin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa