HausaTv:
2025-04-14@16:36:45 GMT

Senegal ta yi Allah-wadai da tsare ‘yan kasarta a Mauritania

Published: 14th, March 2025 GMT

Ministar Harkokin Wajen Senegal, Yacine Fall, ta ce hukumomin kasarta sun bayyana rashin jin dadi game da tsare ‘yan Senegal da kuma tilasta musu barin kasar bisa zarginsu da zama cikin Mauritania ba bisa ka’ida ba.

Hukumomin kasar Mauritaniya sun kaddamar da wani gangamin korar bakin haure daga kasashen Afirka daban-daban.

A wani jawabi da ta gabatar yayin taron amsa tambayoyi a majalisar dokokin kasar ta Senegal kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa Fall ya ruwaito,  “kowace kasa tana da nata dokoki, amma rashin samun takardar zama ko takardar izinin aiki a cikin sa ba zai taba hujja ta cin zarafi ba.

Majalisar dokokin kasar Senegal ta yi kira ga gwamnatin da ta gaggauta daukar matakai don ganin an warware matsalar a’yan kasar da suke zaune a Mauritania,” tana mai bayyana abin da Mauritania ke yi a matsayin “cin zarafin bil’adama.”

A nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar Mauritaniya a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce kasar ta tabbatar da bude kofa ga bakin haure tare da karfafa tare da yin komai a cikin  tsari, da kuma shiga kasar cikin kasar bisa sharudda da suke a a kan doka, tana mai cewa “Mauritaniya tana maraba da baki da ke zama a cikin kasarta bisa doka kuma cikin yanayi mai kyau, musamman wadanda suka fito daga kasashe makwabta.”

Ta kuma yi nuni da cewa, yin kaura ba bisa ka’ida ba a wasu lokuta ya kan zama barazana ga yanayin zaman lafiya da tsaron kasa, a kan haka ne take kokarin tantance yanayin baki mazauna kasar, amma hakan ba zai yi tasiri a kan alakar da ke tsakaninta dad a kasashen dab akin suka fito ba, kuma za a warware batun  ta hanyar fahimtar juna.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Sin Ta Mika Filayen Wasa Da Ta Yi Wa Gyaran Fuska Ga Senegal
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci