Senegal ta yi Allah-wadai da tsare ‘yan kasarta a Mauritania
Published: 14th, March 2025 GMT
Ministar Harkokin Wajen Senegal, Yacine Fall, ta ce hukumomin kasarta sun bayyana rashin jin dadi game da tsare ‘yan Senegal da kuma tilasta musu barin kasar bisa zarginsu da zama cikin Mauritania ba bisa ka’ida ba.
Hukumomin kasar Mauritaniya sun kaddamar da wani gangamin korar bakin haure daga kasashen Afirka daban-daban.
A wani jawabi da ta gabatar yayin taron amsa tambayoyi a majalisar dokokin kasar ta Senegal kamar yadda kamfanin dillancin labaran Faransa Fall ya ruwaito, “kowace kasa tana da nata dokoki, amma rashin samun takardar zama ko takardar izinin aiki a cikin sa ba zai taba hujja ta cin zarafi ba.
Majalisar dokokin kasar Senegal ta yi kira ga gwamnatin da ta gaggauta daukar matakai don ganin an warware matsalar a’yan kasar da suke zaune a Mauritania,” tana mai bayyana abin da Mauritania ke yi a matsayin “cin zarafin bil’adama.”
A nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar Mauritaniya a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce kasar ta tabbatar da bude kofa ga bakin haure tare da karfafa tare da yin komai a cikin tsari, da kuma shiga kasar cikin kasar bisa sharudda da suke a a kan doka, tana mai cewa “Mauritaniya tana maraba da baki da ke zama a cikin kasarta bisa doka kuma cikin yanayi mai kyau, musamman wadanda suka fito daga kasashe makwabta.”
Ta kuma yi nuni da cewa, yin kaura ba bisa ka’ida ba a wasu lokuta ya kan zama barazana ga yanayin zaman lafiya da tsaron kasa, a kan haka ne take kokarin tantance yanayin baki mazauna kasar, amma hakan ba zai yi tasiri a kan alakar da ke tsakaninta dad a kasashen dab akin suka fito ba, kuma za a warware batun ta hanyar fahimtar juna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Me Ya Sa Jama’ar Turai Ke Adawa Da Sayen Kayayyaki Kirar Amurka?
A wani bangare na daban kuwa, dole ne ’yan siyasar Turai su yi tunani cewa, jama’arsu sun dauki irin wannan mataki ne ba ma kawai bisa bukatunsu na sayayya ba, har ma ya kasance mataki ne na nuna adawa da babakeren Amurka, da bukatunsu na dogaro da kansu a bangaren manyan tsare-tsare.
Huldar Amurka da Turai ta wannan fuskar ta yi hannun riga da ainihin ma’anar zumunci, inda lamarin ya yi rauni matuka, kuma tabbas matukar Turai ba ta nemi dogaro da kanta ba, za ta yi asara daga barazana da kalubalen da Amurka take haifarwa. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp