Aminiya:
2025-03-14@13:00:12 GMT

Sojoji sun ceto mutum 7 daga hannun ’yan bindiga a Filato 

Published: 14th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro a Jihar Filato, sun ceto mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace.

An gano mutanen a yankin Ganawuri, da ke Ƙaramar Hukumar Riyom, bayan da sojojin Operation SAFE HAVEN (OPSH) suka kai farmaki maɓoyar ’yan bindigar.

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai

An gudanar da aikin ceton ne a matsayin wani ɓangare na Operation LAFIYAN JAMA’A, wanda ke da nufin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Mai magana da yawun rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya bayyana cewa sojojin sun samu bayanan sirri cewa an ɓoye wasu mutane da aka sace a kusa da hanyar Jos zuwa Ganawuri.

“Yayin farmakin, sojojinmu sun yi arangama da ‘yan bindigar, amma sun tsere bayan sun fuskanci ruwan wuta.

“Daga nan, sojojin suka bi sahu suka kuma ceto mutum bakwai da maharan suka sace,” in ji Manjo Zhakom.

An bayyana sunan mutanen da aka ceto, waɗanda dukkaninsu ‘yan asalin Jihar Bauchi ne: Sale Umar, Muhammadu Inusa, Abdullahi Abdulrasaq, Abdulsalam Muhammad, Muhammad Hamisu, Ibrahim Maradu, da Saidu Sani.

Sojojin sun kuma gano wata jaka mai ɗauke da bargo da kaya da ‘yan bindigar suka bari.

Sun yi wa mutanen da suka ceto tambayoyi don taimakawa musu da bayanan da za su sa a kama ‘yan bindigar da suka tsere.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas

Wata tanka ɗauke da gas ta yi bindiga a Jihar Legas da ke kudu maso yammacin Nijeriya, lamarin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane da jikkata da dama.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata da dare a ƙarƙashin gadar mota ta Otedola, wadda tana daga cikin manyan hanyoyin da ke haɗe Legas da sauran sassan ƙasar.

HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas Ukraine ta amince da ƙudurin tsagaita wuta a fafatawarta da Rasha

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da tankar ke ƙoƙarin juyawa domin kai gas ɗin wani gidan mai, inda a nan ne ta faɗi ta yi bindiga.

Mutane da dama da suka shaida lamarin sun ce ya ƙazanta, sakamakon yadda wuta ta kama motoci da dama da kuma gidaje da ke kusa.

Wakilin kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya tattauna da wani mutum da ya tsira da ransa sakamakon lamarin.

“Tankar ta faɗo kan motata, inda ta tura ta gefen hanya. Sai na yi sauri na gudu bayan na gano cewa gas ne, sai tankar ta yi bindiga cikin ƙasa da minti uku,” in ji Ajayi Segun, wanda ya rasa motarsa ƙirar Sienna sakamakon faruwar lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas, Benjamin Hundeyin, a wani rahoto na wucin-gadi da ya fitar ya tabbatar da cewa lamarin ya rutsa da gidaje huɗu tare da haka kuma motoci 15 sun ƙone ƙurmus.

“Ana zargin hatsarin ya afku ne a lokacin da motar ke kokarin hawan hanyar Legas zuwa Ibadan ta gadar Otedola,” inji shi.

“Saboda haka, motar ta kife a kan hanya sannan ta yi bindiga nan take.”

“Har yanzu ana kididdige adadin rayukan mutanen da aka rasa, domin an gano gawawwaki biyu ne kawai.

“Lamarin ya kuma shafi wani asibiti mai zaman kansa, sai dai har yanzu babu cikakken bayani game da halin da waɗanda lamarin ya shafa a can.

“Za a ci gaba da bayar da rahoto a yayin da ake ci gaba da aikin ceto,” kamar yadda ya bayyana.

Jami’in Hukumar Agajin Gaggawa na Kasa (NEMA) shiyyar Kudu maso Yamma, Ibrahim Farinyole, ya tabbatar da faruwar lamarin da cewa suna ci gaba da ƙididdige asarar da aka yi.

A cewarsa, mutum daya ya mutu yayin da wasu hudu suka jikkata baya ga motoci 14 da shaguna hudu da suka ƙone ƙurmus.

A cikin ‘yan watannin nan, an samu fashewar tankokin mai dama a Nijeriya inda kusan mutum 300 suka rasu a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna
  • Kano: Gobara ta kashe mutum 7 da lalata kadarorin N50m a Fabrairu
  • ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
  • Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum
  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina
  • HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas
  • “Yan Ta’addan Syria Suna Boye Gawawwakin Mutanen Da Su Ka Yi Wa Kisan Gilla