Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Published: 14th, March 2025 GMT
Takawa ta kebantattun kebantattu: sun hada duk abin alkairi na gama-garin mutane, sun hada duk abin alkairi na kebantattu sannan sun kara da nutso da zurfafawa cikin sanin Allah, ba su ganin wanin Allah, a ko da yaushe suna Fadar Allah ko suna Fadar Annabi (SAW) ko suna fadar Waliyyan Allah.
Wadannan Takawa guda Uku, Allah ya fada mana su cikin Alkur’ani yana cewa : “Ba laifi ga wadanda suka yi imani da Allah suka yi aiki mai kyau cikin abin da suka ci, idan suka yi takawa suka yi Imani, sannan suka yi wata takawa kuma suka yi Imani sannan suka yi wata takawa sannan suka yi kyautaye.
Ayar ta sauka ce lokacin da ayar haramta giya ta sauka, sai wasu daga cikin Mu’uminai shubuha ta kama su suke cewa “to yanzun ‘yan uwanmu Muminai da suka sha giya a baya fa, kuma ga shi sun mutu yanzun, to ya za a yi kenan yanzun? Sai Allah ya saukar da wannan ayar yana mai cewa ba laifi a gare su tunda sun mutu lokacin ba a haramta giyar ba.
Alhamdulillah, duk wadannan takawa guda Uku, suna daga cikin falalar Ramadana. Takawa cikin Islam, Takawa cikin Iman sai Takawa cikin Ihsan.
Azumin Ramadana, kwanaki ne kididdigaggu, wata daya ne kacal cikin watanni sha biyu, kuma Allah ya bayyana mana cewa ya san akwai marasa lafiya a cikinmu, kuma akwai matafiya a cikinmu, to sai su kididdige kwanakin da azumin ya tsere musu, su rama a wasu kwanakin.
Ayar da tagabata ta bayyana wajibcin azumin watan Ramadana a Kur’ani, sai kuma hadisi mai zuwa, zai tabbatar da wajibcin azumin watan Ramadana a Sunnah Ta Annabi (SAW).
“An gina musulunci a kan shika-shikai guda biyar: 1- Shaidawa babu wani Ubangiji da ake bautawa da gaskiya sai Allah, da Shaidawa Annabi Muhammad (SAW) Manzon Allah ne 2- Sai Tsaida Sallah, 3 – Ba da Zakka 4- Azumin watan Ramadana 5– Sai Ziyartar Dakin Allah mai girma.”
Ya zo a cikin Hadisin Dalhatu bin Abdullahi, cewa “wani Mutum ya tambayi Annabi (SAW) yana mai cewa ya Ma’aikin Allah, gaya min abin da Allah ya wajabta min na daga azumi, sai Annabi ya ce Watan Ramadana, sai Mutumin Ya kara cewa akwai wani kuma da Allah ya kara wajabta min, sai Annabi ya ce A’a sai dai in za ka yi azumin Nafila.”
Babu jayayya a duk jama’ar musulmi kan wajibcin azumin watan Ramadana.
An wajabta azumin watan Ramadana ranar Litinin, dare biyu da suka shige na watan Sha’aban bayan Hijira. Annabi (SAW) bayan ya yi Hijira zuwa Madina daga Makkah a cikin watan Rabi’ul Awwal, aka tafi zuwa Rabi’us Sani har zuwa Zulhajji, sannan aka juyo Muharram har zuwa Ramadan, a cikin shekara ta biyu kenan da Hijira aka wajabta azumin watan Ramadan.
Alhamdulillah, abin da ya gabata shi ne bayanin azumi daga littafin Allah da Sunnar Annabi Muhammad (SAW) da hadin kan al’ummar musulmi gaba daya cikin wajibcin azumi.
Nasa’i ya ruwaito, Abi Umamata ya ce “Ya Ma’aikin Allah, horar ni da wani aiki kebantacce wanda zan kebanta da shi, sai Manzon Allah (SAW) ya ce, na hore ka da yin azumi, bayan Farillah ka dinga yin na nafila, sabida shi azumi ba shi da kama cikin Ibada.” Sabida kowacce Ibada wasa zai iya shigar ta amma ban da azumi.
Wannan ya nuna alakar Ubangiji da azumi, sabida Ubangiji babu misalinsa kamar yadda azumi sh ima babu misalinsa.
Muslim ya fitar cikin Sahihinsa daga Abi Hurairata ya ce: Manzon Allah SAW Ya ce “Ubangiji Ya ce dukkan Ibada ta Dan’adam ce, sai dai azumi nawa ne, kuma ni ne zan saka masa da wannan. Don ni ya yi, to ni zan saka masa.”
Ya zo cikin Hadisi cewa “Azumi garkuwa ne (tsari ne daga Shaidan, daga wuta, daga dukkan abubuwa masu cutarwa), idan dayanku yana azumi, kar ya fadi maganar da ba ta dace ba, kar ya yi hayaniyar da ba ta dace ba, idan wani ya zage shi ko ya nemi husuma da shi, to ya ce ni mai azumi ne, na rantse da wanda ran Annabi Muhammad (SAW) ke hannunsa, warin bakin mai azumi shi ya fi kamshi ranar Lahira a wurin Ubangiji daga turaren almiski”
Muslim ya fitar cikin Sahihinsa daga Sa’adu ya ce, Manzon Allah (SAW) ya ce: “A cikin Aljannah akwai wata kofa ana kiranta da suna kofar koshi (Rayyanu), ba masu shigar ta sai masu azumi”
Mu sani yaku ‘yan uwa, Allah ya amsa mana azuminmu na Ramadana, Allah ya karfafe mu da wannan kissa cewa, Ma’anar azumi ‘kamewa ko daukakawa’. Azumi ibada ce da babu misalinta kamar yadda Ubangiji ba shi da misali, kowacce ibada cewa ake ‘na yi’ – na yi sallah, na yi zakkah, na yi sadakah na yi… amma azumi sai dai a ce ‘na bari’ – Na bar ci, na bar sha, na bar saduwa da iyali na bar… haka Rabbul izzati shi ma sai dai ka ji babu da, babu iyali, ba ya ci, ba ya sha ba, ba, ba da sauransu.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa cikin yardar Allah.
Alhamdu Lillah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: azumin watan Ramadana wajibcin azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
Jami’an tsaro a kasar Pakistan sun kubutar da mutane 155 daga cikin fasinjoji kimani 450 wadanda yan bindigan daga kungiyar ‘Baloch Liberation Army (BLA) suke garkuawa da su tun jiya, wadanda suka yi barazanar kashesu, idan gwamnatin Islamabad bata biya masu bukatunsu ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar jami’an tsaro na kasar ta Pakisatan na cewa ya zuwa yanzu sun halaka yan bindiga 27. Sannan suna shirin kubutar da sauran nan gaba. Labarin ya kara da cewa daga cikin wadanda aka kubutar akwai mata da yara.
Kafin haka dai a jiya Talata ce yan bindiga na kungiyar BLA suka tsare wani jirgin fasinja mai suna ‘Jaffar Express’ dauke da fasinjoji 450 daga garin Quetta zuwa Peshawar.
Manufar garkuwan dai ita ce neman gwamnatin Pakisatn ta bawa yankin Baluchistan na kasar Pakisatan yencin kanta a matsayin kasa mai zaman kanta.
Labarin ya ce yan bindigan sun ta da nakiya ne suka lalata layin dogon, kafin su tilastawa Jirgin tsayawa.
Ya zuwa yanzu dai yan bindigan sun kashe mutane 3 daga cikin har da direban jirgin.