Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-14@17:07:06 GMT

Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500

Published: 14th, March 2025 GMT

Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500

Ministan kasa a ma’aitar tsaro, Mohammed Bello Matawalle, ya ba magoya bayan jam’iyyar (APC) a jihar Zamfara gudumuwar kudi naira miliyan 500 domin a taimaka musu wajen gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.

 

Mai ba da shawara na musamman kan harkokin siyasa Mattawalle, Alhaji Ibrahim Danmalikin Gidan Goga ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau.

 

A cewar Gidan-Goga, Ministan ya zabi bayar da kudi ne maimakon kayan abinci, saboda tuni wasu ‘yan siyasa a jihar suka raba wa magoya bayansu hatsi.

 

Ya kuma jaddada cewa tallafin kudi zai baiwa magoya bayan jam’iyyar APC damar siyan wasu muhimman abubuwan da ake bukata a cikin watan Ramadan.

 

“A wannan karon, maimakon ba wa jama’a hatsi iri-iri, Ministan ya yanke shawarar bayar da tsabar kudi saboda wasu ‘yan siyasa sun riga sun raba kayan abinci,” ya bayyana.

 

Ya ci gaba da cewa, tsohon Gwamna Sanata Abdul Aziz Yari ya bayar da gudummawar tireloli na hatsi iri-iri 496, wanda hakan ya sa Ministan ya kara wannan kokari da tallafin kudi.

 

Gidan-Goga ya bayyana cewa, mutane 200 daga kowace karamar hukuma 14 da ke Zamfara sun karbi ₦100,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 280.

 

“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 24 daga kananan hukumomi biyar na shiyyar Sanatan Zamfara ta Yamma sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 30.”

 

“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 90 daga kananan hukumomin jihar Zamfara ta tsakiya da kuma ta Zamfara ta Arewa sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 22.5.”

 

Sauran nau’ikan wadanda suka ci gajiyar kuma sun sami kudade a matsayin wani bangare na kunshin jin dadin Ramadan na Minista.

 

Gidan-Goga ya tabbatar da cewa sama da kashi 80 cikin 100 na wadanda aka yi niyya sun karbi kudadensu.

 

Ya lura cewa wadanda suka amfana daga Bakura, Gummi, Kaura-Namoda, Maradun, Shinkafi, da Talata-Mafara duk sun tattara kudadensu.

 

Sai dai kawo yanzu mutum 100 da suka ci gajiyar tallafin daga kananan hukumomin Tsafe, Zurmi, Bungudu, Bukkuyum, da Anka ne kowannensu ya karbi nashi kason, yayin da sauran wadanda suka ci gajiyar shirin za a biya su nan gaba kadan.

 

Ya kara da cewa har yanzu wadanda suka ci gajiyar tallafin daga karamar hukumar Birnin Magaji ba su samu kudadensu ba sakamakon tsaikon da aka samu wajen gabatar da jerin sunayen wadanda suka karba.

 

 

 

AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Matawalle Zamfara da suka ci gajiyar wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

Daga karshe ta ce da farko ta samu turjiya daga wajen wasu mutane a kan kudurinta na fara harkar fim amma kuma ta yi biris dasu ta fara, amma kuma yanzu wadanda a baya ke hanata shiga fim su ne yanzu ke yi mata murnar samun nasara hakan ya matukar bata mamaki, duba da cewar wadanda ta ke tunanin za su tsaneta kasancewarta jarumar fim sun zamo masoyanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13