Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Samar da Dokar Shirye-Shiryen Matasa Da Ayyukan

 

Ministan ci gaban matasa, Ayodele Olawande, ya jaddada kudirin gwamnatin tarayya na karfafa matasa domin samar da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin kasar nan.

 

Ministan ya ce ziyarar da ya kai jihar Sokoto na da nufin kara cudanya da matasa a cikin watan Ramadan da bayar da tallafi mai mahimmanci.

 

Olawande, wanda ya samu rakiyar Seyi Tinubu, ya jaddada mahimmancin shirye-shiryen da suka shafi matasa, ciki har da samar da dandalin tattaunawa kan ci gaban matasa na kasa.

 

Ya yi nuni da cewa, shugaban kasa Bola Tinubu da Gwamna Ahmed Aliyu suna da manufa daya na ci gaban matasa, ta yadda za a yi amfani da albarkatun da aka ware wa Sokoto yadda ya kamata.

 

Ministan ya kuma yaba da bullo da shirin ba da lamuni na dalibai, inda ya bayyana shi a matsayin wani gagarumin shiri na tallafawa daliban Najeriya.

 

Ya kuma ba da tabbacin cewa, akwai wasu shirye-shiryen da suka shafi matasa, inda Sokoto za ta ci gajiyar muhimman tsare-tsare a fannin noma, gidaje, da kuma shirye-shiryen horarwa.

 

Ya kuma kara ba da tabbacin cewa FG na kokarin samar da yanayi mai dacewa da matasan Najeriya za su ci gaba.

 

A nasa jawabin, gwamna Ahmed Aliyu na sokoto, ya bayyana ziyarar a matsayin wata shaida ga jajircewar da gwamnatin ta yi wajen karfafa matasa.

 

Ya yabawa Seyi Tinubu, wanda shine wanda ya assasa Renewed Hope Youth Empowerment Initiative, bisa gudunmawar da yake bayarwa a harkokin siyasa da ci gaban tattalin arziki, yana mai kira gare shi da ya mika shirye-shiryensa ga matasan Sokoto.

 

Gwamnan ya kuma bayyana irin kokarin da gwamnatin sa ke yi na tallafa wa matasa da suka hada da nada matasa a manyan mukamai a gwamnati da samar da ilimi kyauta ga dukkan dalibai ba tare da la’akari da addini ko kabila ba.

 

Ya yabawa Tinubu kan irin ayyukan alheri da yake yi a cikin watan Ramadan, musamman ga marasa galihu.

 

Tun da farko, Seyi Tinubu ya bayyana kudirinsa na ci gaban matasa a Sakkwato, inda ya yi alkawarin cewa gidauniyarsa za ta ci gaba da tallafa wa ayyuka a fadin kananan hukumomin jihar 23.

 

Nasir Malali

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran babban titin Abuja-Kaduna-Zariya-Kano, wadda ke da matukar muhimmanci ga tattalin arzikin Arewacin Najeriya.

Da yake jawabi a taron kaddamarwar a Kagarko, Jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani, ya bayyana yadda aka yi watsi da hanyar da kuma irin mummunan tasirin da hakan ya yi ga rayuka da ci-gaban tattalin arziki.

Gwamna Uba Sani, ya yaba wa Tinubu bisa farfado da aikin, yana mai nuni da muhimmancin hanyar a matsayinta na mafi yawan zirga-zirgar ababen hawa a Arewa.

Da yake ba da tabbacin kamma aikin a cikin watanni 14, Tinubu wanda Ministan Ayyuka, Sanata David Umahi, ya ce za a gina titin ne da kankare, kamar babbar hanyar Legas zuwa Kalaba.

An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Ministan ya kara da cewa aikin zan dangana har zuwa filin jirgin sama na Kano, kuma za a sanya kyamarorin CCTV gaba daya a tsawon titin, wanda sabon dan kwangila ne zai aiwatar.

Ya ce, shugaban kasa ya amince da naira biliyan 252 don muhimman sassan aikin, inda aka riga aka biya kashi 30%, yanan mai yaba muhimmiyar rawar da Gwamna Uba Sani ya taka a aikin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock