Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-14@12:58:27 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Published: 14th, March 2025 GMT

Likitoci Sun Shawarci Jama’a Su Rika Zuwa Asibiti Akai-Akai

Babban magatakarda, sashin Nephrology, Federal Teaching Hospital Gombe (FTHG), Dr. Fidelis Linga ya bukaci jama’a da su rungumi salon rayuwa mai inganci domin hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a Gombe a yayin bikin ranar ciwon koda ta duniya.

 

Dokta Fidelis Linga ya bayyana halaye marasa kyau kamar yawan shan barasa, shan taba, cin abinci mara kyau, da kuma salon rayuwa a matsayin abubuwan da ke haifar da hauhawar cututtukan da ke da alaƙa da koda.

 

Ya kuma jaddada mahimmancin ziyarar asibitoci akai akai, da daidaita tsarin abinci, da motsa jiki a kai a kai wajen hana kamuwa da cutar koda.

 

Ya bayyana cewa a duniya baki daya, mutane miliyan 850 ne ke fama da cutar koda wanda miliyan 11 daga ciki ke mutuwa daga cutar a duk shekara yana mai bayyana yanayin a matsayin abin damuwa.

 

Dokta Fidelis Linga ya ce FTH Gombe na kokarin samar da karin injinan wankin koda wato dialysis da ma’aikatan lafiya don biyan bukatun dimbin masu cutar koda da ke zuwa wurin aikin wankin.

 

Ya ce an yi ƙoƙarin ne don inganta hanyar yin amfani da dialysis na ceton rai ga majinyata da ke fama da cututtukan koda.

 

HUDU Shehu/Gombe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata

Jami’an tsaro a kasar Pakistan sun kubutar da mutane 155 daga cikin fasinjoji kimani 450 wadanda yan bindigan daga kungiyar ‘Baloch Liberation Army (BLA) suke garkuawa da su tun jiya, wadanda suka yi barazanar kashesu, idan gwamnatin Islamabad bata biya masu bukatunsu ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar jami’an tsaro na kasar ta Pakisatan na cewa ya zuwa yanzu sun halaka yan bindiga 27. Sannan suna shirin kubutar da sauran nan gaba. Labarin ya kara da cewa daga cikin wadanda aka kubutar akwai mata da yara.

Kafin haka dai a jiya Talata ce yan bindiga na kungiyar BLA suka tsare wani jirgin fasinja mai suna ‘Jaffar Express’ dauke da fasinjoji 450 daga garin Quetta zuwa Peshawar.

Manufar garkuwan dai ita ce neman gwamnatin Pakisatn ta bawa yankin Baluchistan na kasar Pakisatan yencin kanta a matsayin kasa mai zaman kanta.

Labarin ya ce yan bindigan sun ta da nakiya ne suka lalata layin dogon, kafin su tilastawa Jirgin tsayawa.

Ya zuwa yanzu dai yan bindigan sun kashe mutane 3 daga cikin har da direban jirgin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi
  • Kasar Sin Ce Ke Kan Gaba A Matsayin Kasar Da Ta Fi Samun Jari Daga Ketare
  • An Bukaci Jama’a Su Rika Binciken Lafiyarsu Don Kare Kai Daga Cutar Koda
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa  Tehran
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Sun Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Cutar Sanƙarau Ta Kashe Mutum 26, 248 Sun Kamu A Kebbi
  • “Yan Ta’addan Syria Suna Boye Gawawwakin Mutanen Da Su Ka Yi Wa Kisan Gilla
  • Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato