Leadership News Hausa:
2025-04-14@20:44:45 GMT

2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa

Published: 14th, March 2025 GMT

2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa

Wannan lamari ci gaban da haifar da zazzafar martani daga jam’iyyun adawa da manazarta siyasa wadanda suka yi zargin cewa hakan ya saba wa dokar zabe da kundin tsarin mulkin 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima.

Masana harkokin shari’a da masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa irin wannan kamfen da ba a kai ba, yana kawo cikas ga dimokuradiyya, da bin doka da oda da kuma tsarin zabe.

A watan da ya gabata ne jam’iyyar APC ta kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa, Tinubu da Gwamna Nasir Idris a Jihar Kebbi as zaben 2027.

Taron wanda aka gudanar a babban filin wasa na garin Birnin Kebbi, ya samu halartar ministan kasafi da tsare-tsare na tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu da Gwamna Nasir Idris da dan majalisar wakilai kuma abokin Tinubu, James Abiodun Faleke da karamin ministan ilimi, Yusuf Tanko Sununu da sauran shugabannin APC.

Bayan taron na Kebbi, shugabannin jam’iyyar APC, da suka hada da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Ajibola Basiru da ministan noma, Abubakar Kyari da wasu da dama sun lalubo yadda Tinubu zai sake tsayawa takara a yayin wani shirin bunkasa noma da jarin Dan’adam wanda Sanata Saliu Mustapha ya shirya a Ilorin na Jihar Kwara.

Makonnin da suka gabata, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kaduna sun amince tare da gamsuwa ga Shugaba Tinubu da Gwamna Uba Sani, “Saboda jagorancinsu da manufofin da suka dace da jama’a.”

A wata sanarwa da ya fitar, sakataren jam’iyyar a jihar, Yahaya Baba Pate, ya ce masu ruwa da tsaki sun ba da goyon baya ne a taron da aka gudanar a ofishin kula da Jihar Kaduna da ke Abuja. Wannan ya biyo bayan goyon bayan shugabannin biyu na kara yin wa’adin mulki a karo na da daukacin kansiloli 255 na jihar suka amince da shi.

A karshen mako, a lokacin biki da Ganduje da Sanata Barau Jibrin suka tsara, wasu daga cikin kungiyoyin masu goyon bayan Atiku Abubakar, daga jihohi 19 na arewa, yayin da suke sanar da sauya shekarsu zuwa APC sun yi alkawarin aiki don ci gaban gwamnatin Tinubu a 2027.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’ila Bagaei ya godeawa ministan harkokin wajen kasar Omman kan yadda ya shirya ya kuma gabatar da tattaunawa tsakanin JMI da Amurka a birnin Mascat da kuma kai kawon da yayi a  tsakanin bangarorin biyu.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Bagaei yana bayyana haka a wani sakon da ya aika a cikin shafinsa na X  a jiya Asabar, ya kuma aika da sakon ne a dai dai lokacinda ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana kan hanyarsa ta dawowa Tehran, bayan tattaunawar. Ya kuma kara da cewa yana fatan Badr bin Hamad Al Busaidi zai ci gaba da wannan kokarin a ranar Asabar mai zuwa inda bangarorin biyu zasu sake haduwa, sannan har zuwa karshen tattaunawar. Bayan kammala tattaunawar dai,  shugaban tawagar JKI a tattaunawar kuma ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana a shafinsa na X kan cewa, tattaunawar ta yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje