Aminiya:
2025-03-14@12:56:59 GMT

Wadda ke damfara da sunan matar gwamnan Katsina ta shiga hannu

Published: 14th, March 2025 GMT

Hukumar EFCC ta kama wata mata da mijinta bisa zargin yin sojan gona da sunan mai ɗakin Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Radda, wajen damfarar kuɗi Naira miliyan 197.75.

An gurfanar da su a gaban babbar kotun Jihar Kaduna, tare da wasu mutum biyu da ake zargi suna taimaka musu wajen aikata laifin.

’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3 NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Ta A Najeriya

EFCC ta ce mutanen huɗu sun haɗa kai wajen amfani da sunan Hajiya Fatima Dikko Radda don samun canjin dala daga wani mai sana’ar canji.

Matar ta gabatar da kanta a matsayin Fatima Dikko Radda, tana buƙatar a yi mata canjin dala.

Mijinta kuma ya samar da layukan waya da aka yi wa rajista da sunan Fatima Dikko Radda, domin a rikita tunanin mai amfani da manhajar ‘True Caller’.

Bayan matar ta nemi a yi mata canjin dala, sai suka turawa mai canjin lambar asusun banki da zai tura kuɗin kafin ta aika masa da dalar.

Da farko, ta karɓi Naira miliyan 89 daga hannun wani mutum mai suna Aminu Usman, da nufin za ta tura masa dala 53,300.

Daga baya kuma, ta sake karɓar Naira miliyan 108, tana mai cewa za ta tura masa dala 118,000.

EFCC na ci gaba da bincike kan lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara Uwargidan Gwamnan Katsina Fatima Dikko Radda

এছাড়াও পড়ুন:

 Uganda ta tura dakaru na musamman zuwa babban birnin Sudan ta Kudu

Rundunar sojan Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman domin tabbatar da tsaro a babban birnin Sudan ta Kudu bisa bukatar Juba, a daidai lokacin da ake fargabar sake barkewar yakin basasa, musamman a halin da ake ciki tsakanin shugaban Sudan ta Kudu da mataimakinsa na farko.

A wannan Talata rundunar sojin Uganda ta sanar da tura dakaru na musamman zuwa Juba, babban birnin Sudan ta Kudu.

Kakakin rundunar sojin Uganda Felix Kulayigye ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, batun tura sojojin na zuwa ne bisa bukatar gwamnatin Sudan ta Kudu.

An kara samun tashin hankali a ‘yan kwanakin nan a kasar Sudan ta Kudu mai arzikin man fetur, bayan da gwamnatin shugaba Salva Kiir ta kame wasu ministoci biyu da wasu manyan jami’an soji da ke kawance da mataimakin shugaban kasar na farko Riek Machar. Tuni dai aka saki minista guda.

Kamen da aka yi a Juba da kuma kazamin fadan da ya barke a kusa da garin Nasir na arewacin kasar ana ganin zai kawo cikas ga yarjejeniyar zaman lafiya ta shekarar 2018 da ta kawo karshen yakin basasa na tsawon shekaru biyar tsakanin dakarun da ke biyayya ga Kiir da Machar inda aka kashe kusan mutane 400,000.

Bayan barkewar yakin basasa a Sudan ta Kudu a shekara ta 2013, Uganda ta aike da dakarunta zuwa Juba domin tallafawa dakarun Kiir da ke yaki da Machar. Daga karshe dai sojojin Uganda sun janye a shekarar 2015. An sake tura sojojin Uganda zuwa Juba a shekara ta 2016 bayan da aka sake gwabza fada tsakanin bangarorin biyu, amma kuma aka janye su daga bisani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sama da ‘Yan Mata 74,000 Suka Amfana Shirin AGILE Cash A Kano
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • Peter Obi ya yi ganawar sirri da gwamnan Bauchi
  • Fiye Da Yara Mata 74,000 Sun Amfana Da Shirin Tallafin Kudi Na AGILE A Kano
  • Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi
  • Uwargidan Tinubu Ta Bai Wa Mata Manoma Tallafin Naira Miliyan 26 A Nasarawa
  • Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro
  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina
  •  Uganda ta tura dakaru na musamman zuwa babban birnin Sudan ta Kudu