Leadership News Hausa:
2025-03-14@12:56:59 GMT

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

Published: 14th, March 2025 GMT

Manchester United Ta Kai Zagayen Gaba Na Gasar Europa League 

A makon da ya gabata Manchester United ta buga canjaras a wasan da Real Sociedad na gasar Europa League zagaye na farko a filin wasa na Reale Arena dake Sen Sebastian.

Amma Man Utd ɗin ta gasgata abinda bahaushe ke cewa kowa a gidansa Sarki ne bayan ta zazzagawa Sociedad ƙwallaye 4 a raga, da kuma wannan sakamakon ne United wadda Ruben Amorim ke jagoranta ta tsallaka zuwa matakin na kusa da na kusa da na karshe a gasar ta Europa League.

Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028 Bayan Shekaru 115 Manchester United Za Ta Gina Sabon Filin Wasa

Kyaftin din masu masaukin baƙin Bruno Fernandes ne ya zura ƙwallaye uku rigis a wasan kafin Diogo Dalot ya jefa ta huɗu, duk da cewar United ɗin aka fara jefa wa ƙwallo a raga amma hakan bai sa sun yi sanyin gwuiwa a Old Trafford ba.

Yanzu Manchester United za ta hadu da Olympic Lyon ta ƙasar Faransa a wasan zagayen na kusa da na ƙarshe da za a buga ranar 10 ga watan Afrilu mai kamawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Bayan ɗimbin falala da yawan samuwar ibadun da ke ƙara kusanta bayi ga Ubangijinsu, da azumin watan Ramadan ke zuwa da shi kamar yadda malamai suka saba faɗa, Hakazalika kuma a watan na zuwa da wata al’ada mai ɗimbin tarihi da ke ɗebe wa al’umma musamman na Arewacin Najeriya kewa.

Wannan al’adar ita ce ta tashe da ake fara d zarar watan azumi ya kai kwanaki 10.

DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

Maza da mata na gudanar da wannan al’ada ta hanyar yin shigar kwaikwayo tare da ɓatar da kama, su ringa zagayawa gidaje da kwararo-kwararo ɗauke da ganga da kayan kaɗe-kaɗe suna bugawa suna waƙa.

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan wannan daɗaɗɗiyar al’adar, don jin inda ta samo asali, tarihinta da kuma yadda ake gudanar da ita.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Cire Maguire Cikin Tawagar Ingila Da Za Ta Buga Wasan Neman Gurbi
  • 2027: An Buga Gangar Neman Tazarcen Tinubu A Arewa
  • ’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina
  • Peter Obi ya kusa dawowa APC — Hadimin Tinubu
  • DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?
  • Matsin Amurka Ya Zama Zaburarwa Ga Kasar Sin Wajen Kara Samun Ci Gaba
  • Barcelona Ta Tsallaka Zuwa Matakin Kwata Fainal A Gasar Zakarun Turai 
  • Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato
  • Bayan Shekaru 115 Manchester United Za Ta Gina Sabon Filin Wasa