‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’
Published: 14th, March 2025 GMT
Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ke yi, tana yi ne da nufin gyara makomar yara masu tasowa.
Yayin da yake jawabi ga kungiyar ‘Yan majalisa ta uku – wadda ya kasance cikin a Jamhuriya ta uku – da suka kai masa ziyara a fadarsa, Shugaba Tinubu ya ce a baya kasar na kashe kudaden yaran kasar da ba a kai ga haihuwarsa ba.
“Shekara 50 da suka gabata, Najeriya na kashe kudaden yaran da ba a kai ga haihuwarsu ba, tare da mayar da hankali kan man fetur wajen samun kudin shiga. Ba a yi wani tsari na tallafa wa yaran da za a haifa a gaba ba,” kamar yadda ya ce.
Shugaban ya kuma bayyana tarin matsalolin da ya fuskanta a farkon mulkinsa, musamman fannin tattalin arzikin da rayuwar jama’a.
“Mun fuskanci tarin kalubale a lokacin da na karbi mulki. Inda ba mu dauki matakai ba da yanzu kasar ta talauce, kuma ai hakkinmu ne mu kare tattalin arzikinmu daga rugujewa”, in ji Shugaba Tinubu.
To amma shugaban ya ce a yanzu kwalliya ta fara biyan kudin sabulu dangane da sauye-sauyen da gwamatinsa ta fara ɓullo da su.
“Amma a yau bayan shimfida mai kyau da muka yi, mun smau nasarar magance matsalolin da suka tunkaro kasarmu, a yanzu canjin kudi ya daidaita, farashin abinci na ci gaba da sauka, musamman a lokacin Ramadan, da yardar Allah wahalar ta zo karshe”, a cewar shugaban kasa.
Bello Wakili/Abuja
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna
Wasu ’yan bindiga da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu ’yan ƙauye su goma daga wasu unguwanni uku da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Larabar, da misalin ƙarfe 2 na tsakar dare inda wasu gungun ’yan bindiga suka kai farmaki a unguwar Unguwan Yashi-Maraban Kajuru tare da yin garkuwa da mutane shida.
Kano: Gobara ta kashe mutum 7 da lalata kadarorin N50m a Fabrairu Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — ObasanjoWaɗanda aka sace su ne: God-Dream Ladan, Lady God-Dream, Philip Mudakas, Mercy Philip, Bitrus Philip, da Gmen Philip.
Hakazalika, a ƙauyen Makyali, wasu mutane biyu sun samu raunuka na harbin bindiga, kuma a halin yanzu ana jinyarsu a asibitin Maraban Kajuru bayan ’yan bindiga sun kai wa unguwar hari.
An kuma yi garkuwa da wasu mata biyu Rahina Yahaya da Zulai Yahaya a ƙauyen. Waɗanda suka jikkata dai sun haɗa da: Ubale Yahaya da Abdullahi.
An samu rahoton cewa gungun ’yan bindigan sun koma Ungwan Mudi Doka da misalin ƙarfe 4 na asubahi inda suka yi garkuwa da wasu mutane biyu – Amos Michael da Samita Amos.
Muƙaddashin Hakimin Kufana, Stephen Maikori ya tabbatarwa Aminiya faruwar lamarin a ranar Alhamis, inda ya ce a baya-bayan nan an samu raguwar kai hare-haren, amma kuma a cikin makon nan ne suka sake kunno kai.
“Ya zuwa yanzu, an tafi da mutane goma, yayin da biyu suka samu raunuka, yanzu suna karɓar magani. Muna roƙon a ƙara ɗaukar matakan tsaro cikin gaggawa da ɗaukar matakin ceton rayuka da dukiyoyi a cikin wannan yankin,” in ji shi.
Ya kuma ƙara da cewa an kai rahoton faruwar lamarin ga hukumomin tsaro a kan lamarin. A halin da ake ciki dai har yanzu gwamnatin jihar da rundunar ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, an kasa samunsa ta wayar tarho har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.