A yau Juma’a ne aka bude taron kasashen Iran, Rasha da China, a matakin mataimakan ministocin harkokin waje inda su ka tattauna shirin makamashin Nukiliya na Iran. Mahalarta taron sun bukaci ganin an dauke wa Iran takunkuman da aka kakaba mata, sannan kuma a warware batun shirinta na makamashin Nukiliya ta hanyar tattaunawa.

Kasashen na China, Rasha da kuma Iran sun bayyana takunkuman na Amurka akan Iran da cewa, ba halartattu ba ne.

Haka nan kuma sun ce; Tuntubar juna da kuma tattaunawar diplomasiyya bisa girmama juna ne kadai zabin da ake da shi domin cimma manufa.

Taron da aka yi a yammacin birnin Beijing ya kunshi mataimakan  ministan harkokin wajen Iran  Garid Ridh Abadi, Sai Rasha  Sergey Ryabkov da kuma mai masaukin baki na China  Ma Zhaoxu.

A daya gefen kasashen uku sun tattauna hanyoyin bunkasa alaka a tsakaninsu a karkashin kungiyoyin kungiyoyin “Shanghai” da kuma “Brikcs”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar

Kwamandan sojojin kasa na JMI Laftanar-Janar Kiyomars Haydari ya bada sanarwan cewa; A bisa umranin jagoran juyin musulunci Imam Sayyid Ali Khamnei , sojojin kasa na JMI suna cikin shirin ko ta kwana domin mayar da martani akan kowace irin barazana ga tsaron kasar.

Laftanar janar Haidari ya kuma ce: A halin yanzu da akwai rundunoni 11 da su ke cikin shiri a kan iyakoki kasar domin sanya idanu da tattara bayanai saboda tabbatar da tsaron kasar.

Kwamandan sojan kasa na Iran ya kuma ce; Saboda sojojin suna cikin shirin ko-ta-kwana ne, barazanar da ake fuskanta ta zagwanye, da hakan ya ke a matsayin kandagarko.

Har’ila yau Laftanar janar Haidari ya yi ishara da rawar dajin da sojojin kasa su ka yi, har sau uku a cikin shekarar hijira Shamshiyya ta 1403. Sannan da wadanda za su a sabuwar shekara da za ta shigo.

Ya ce za’a gudanar da wani atisayen wanda zai da ce da girman barazanar da ake fuskanta.

Haidari ya kammala da cewa a sabuwar shekarar Iran da za a shiga, za ta zama ta kara yawan karfin tsaron kasar ne, domin takawa makiya birki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta
  • Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar
  • ECOWAS ta kaddamar da rundunarta mai dakaru 5,000 don yakar ta’addanci
  • Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa  Tehran
  • Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
  • Pezeshkian: Babu Batun Tattaunawa Da Amurka A Karkashin Matsin Lamba
  • Sharhin Dangane da: Atisayen Damarar Tsaro Ta 2025 Tsakanin Kasashen China, Rasha Da Iran
  •  Ukraniya Ta Hai Wa Birnin Moscow Hari Da Jirage Marasa Matuki
  • Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Rufe Zaman Taronta Na Shekara-shekara