Karancin Man Fetur A Jamhuriyar Nijar Yana Damun ‘Yan Kasa
Published: 14th, March 2025 GMT
An kusa shiga mako guda daga lokacin da aka fara fuskantar karancin mai a gidajen man fetur da hakan ya jefa masu ababan hawa cikin damuwa.
Rabon man fetur da kamfanin SONIDEP yake yi bai wadatar da masu abubuwan hawa ba, yana kuma kawo cikas a harkokinsu na yau da kullum.
Da akwai dalilai da dama da su ka haddasa karancin man fetur din, sai dai al’ummar kasar suna son ganin mahukunta sun fito fili sun yi musu bayanin abinda yake faruwa.
Wani mazaunin birnin Yemai Assoumane Hamadou suley ya fada wa manema labaru cewa; Ba mu da cikakken bayani akan abinda yake faruwa, domin mahukanta da ya kamata su fito su yi bayani, ba su yin hakan.
Su kuwa matukan motocin Tasi (SYNCTAXITU), cewa su ka yi, ya kamata gwamnati ta kara yawan man fetur da ake hakowa a kowace rana.
Babban sakataren kungiyar matuka Tasi din Agali Ibrahim cewa ya yi, “ Idan aka fada mana cewa da akwai manyan motocin jigilar man fetur 25 da ake bai wa birnin Niamey, to abinda zan fada musu shi ne cewa bai isa ba.”
Haka nan kuma ya yi ishara da fasakwaurin man fetur din da ake yi da yana daga cikin dalilin karancinsa da ake fuskanta.
Da akwai shirin kara yawan tankokin mai daga 25 zuwa 100 da za a rika bai wa babban birnin ka kowace rana.
Ba kasafai ake shiga irin wannan yanayin ba a jamhuriyar Nijar wacce take da arzikin mamn fetur da aka fara hako shi tun a wajajen 2011.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Babu Batun Tattaunawa Da Amurka A Karkashin Matsin Lamba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi kakkausar suka ga matakin da gwamnatin Trump ya dauka kan Iran, yana mai bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba Ukraine ba ce, kuma ba za ta yi shawarwari da Amurka bisa barazana ko tilasci ba.
“Dole ne mu kiyaye dangantaka da duniya. Ba ma son mu yi sabani ko jayayya da kowa, amma hakan ba yana nufin za mu durkusa cikin wulakanci a gaban kowa ba,” in ji Pezeshkian yayin wani taron kungiyar ‘yan kasuwan Iran a Tehran a ranar Talata.
“Muna iya mutuwa da daraja, amma ba za mu taɓa rayuwa cikin kunya da kaskanci ba.”
Pezeshkian ya yi watsi da abin da ya bayyana a matsayin wa’adi daga Donald Trump, yana mai nuni da wata wasika da aka ce shugaban Amurka ya aike zuwa Iran.
Wasikar ta bukaci Tehran da ta dakatar da shirye-shiryenta na nukiliya da makamai masu linzami da kuma daukar wasu matakai domin samun sassaucin takunkumi.
Ya soki Trump da rashin mutunta takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelensky, yayin da ya matsa masa lamba kan ya amince da wata yarjejeniya da Rasha.
Shugaban na Iran ya ce halin da Trump ya nuna a ganawarsa da Zelensky a fadar White House abin kunya ne.