Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-15@01:53:02 GMT

Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya

Published: 14th, March 2025 GMT

Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya

Gwamnatin mulkin sojin Sudan ta ayyana haramta duka kayayyakin da aka shigar da su ƙasar daga Kenya, a wani mataki na martani karɓar baƙuncin RSF da ƙawayenta da Nairobin ta yi.

Ministan kasuwancin Sudan, ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar, majalisar ikon ƙasar, wadda ta zargi Kenya da rura tashin hankali a Sudan.

A ganawar da aka yi a Nairobi ce, RSF ta yanke shawar kafa gwamnatin ƴan adawa a wuraren da take iko da su tare da sanya hannu kan abin da ta kira ‘rubuta kundin tafiyar gwamnatin’.

Sudan ce ƙasa ta 10 a duniya, sannan ta biyu a Afirka, cikin jerin ƙasashen da suka fi sayen ganyen shayin Kenya.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kenya

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan

Kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hamas ta yi gargadi akan cewa; Wata sabuwar yunwa za ta  bulla a Gaza saboda yadda HKI take ci gaba da killace yankin da hana shigar da kayan agaji hatta a cikin watan Ramadan.

Kakakin kungiyar ta Hamas Abdullatif al-Qa’uni wanda ya fitar da wani bayani ya ce; Falasdinawa a yankin Gaza an killace su, makonni biyu a jere, kuma sojojin mamaya sun hana a shigar da kayan abinci,magunguna, da makamashi, wanda hakan yake a matsayin amfani da yunwa a matsayin makamin.

Qa’ani ya kara da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne jefa Falasdinawa cikin yunwa. Haka nan kuma ya ce;  A nan gaba kadan kayakin da ake da su na bukatun yau da kullum za su kare a cikin Gaza, wanda hakan zai kara wahalar da mutanen yankin.

Kakakin kungiyar ta Hamas ya kuma yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su yi matsin lamba akan HKI domin bude iyakoki da bayar da damar shigar da kayan agaji.

Tun a farkon wannann watan Maris da muke ciki ne HKI ‘yan mamayar su ka hana shigar da muhimman kayakin da ake bukata zuwa cikin yankin na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasar Sin Ta Yi Alƙawarin Ƙarfafa Hulɗar Da Ke Tsakaninta Da Kano
  • Hamas Ta Yi Gargadin Bullar Yunwa A Gaza A Cikin Watan Ramadan
  • 2027: Na Shirya Tsaf Don Yin Aiki Tare Da Peter Obi Don Ceto Ƙasar Nan, Gwamnan Bauchi
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Wajen Inganta Noma, Sufuri Da Ma’adanai 
  • Gwamnatin Bahrain Ta Kara Kaimi Wajen Kama Yan Adawa Daga Ciki Har Da Yara Kanana
  •  Uganda ta tura dakaru na musamman zuwa babban birnin Sudan ta Kudu
  • Hamas : matakin Isra’ila na hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza ”laifi na yaki”ne
  • DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?
  • DAGA LARABA: Ko Kun San Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?