Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-14@16:20:26 GMT

Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya

Published: 14th, March 2025 GMT

Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya

Gwamnatin mulkin sojin Sudan ta ayyana haramta duka kayayyakin da aka shigar da su ƙasar daga Kenya, a wani mataki na martani karɓar baƙuncin RSF da ƙawayenta da Nairobin ta yi.

Ministan kasuwancin Sudan, ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar, majalisar ikon ƙasar, wadda ta zargi Kenya da rura tashin hankali a Sudan.

A ganawar da aka yi a Nairobi ce, RSF ta yanke shawar kafa gwamnatin ƴan adawa a wuraren da take iko da su tare da sanya hannu kan abin da ta kira ‘rubuta kundin tafiyar gwamnatin’.

Sudan ce ƙasa ta 10 a duniya, sannan ta biyu a Afirka, cikin jerin ƙasashen da suka fi sayen ganyen shayin Kenya.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kenya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran

Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.

Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.

Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasar
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi