An Cire Maguire Cikin Tawagar Ingila Da Za Ta Buga Wasan Neman Gurbi
Published: 14th, March 2025 GMT
Sabon kocin Ingila, Thomas Tuchel ya cire ɗan wasan bayan Ingila Harry Maguire cikin jerin ƴanwasan Ingila da za su buga wasannin neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026.
Cikin jerin ƴan wasa 26 da sabon kocin ƙasar Thomas Tuchel ya fitar, ranar Juma’a ya sanar da sunan Marcus Rashford bayan cire shi a wasannin baya.
Haka ma kocin ya saka sunan tsohon ɗan wasan Liverpool da ke taka leda a ƙugiyar Ajax, Jordan Henderson cikin tawagar.
A karon farko mai tsaron ragar Burnley, James Trafford da ɗan wasan bayan Liverpool, Jarell Quansah za su iya samun damar buga wa babbar tawagar Ingila ƙwallo ba a ke cikin tawagar
A ranar Juma’a, 21 da watan Maris ne tawagar Ingila za ta ƙarbi baƙuncin Albania a filin wasa na Wembley, kafin ranar Litinin 24 ga watan na Maris ta kara da ƙasar Latvia a wasannin neman gurbin.
Ga jerin ƴan wasan 26 ga Thomas Tuchel ya fitar domin fafatawa a wasannin.
Masu tsaron raga: Dean Henderson (Crystal Palace), Jordan Pickford (Everton), Aaron Ramsdale (Southampton), James Trafford (Burnley)
Ƴanwasan baya: Dan Burn (Newcastle United), Levi Colwill (Chelsea), Marc Guehi (Crystal Palace), Reece James (Chelsea), Ezri Konsa (Aston Villa), Myles Lewis-Skelly (Arsenal), Tino Livramento (Newcastle United), Jarell Quansah (Liverpool), Kyle Walker (AC Milan, loan from Manchester City)
Ƴan wasan tsakiya: Jude Bellingham (Real Madrid), Eberechi Eze (Crystal Palace), Jordan Henderson (Ajax), Curtis Jones (Liverpool), Cole Palmer (Chelsea), Declan Rice (Arsenal), Morgan Rogers (Aston Villa)
Ƴan wasan gaba: Jarrod Bowen (West Ham United), Phil Foden (Manchester City), Anthony Gordon (Newcastle United), Harry Kane (Bayern Munich), Marcus Rashford (Aston Villa, loan from Manchester United), Dominic Solanke (Tottenham Hotspur)
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasanni
এছাড়াও পড়ুন:
DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Bayan ɗimbin falala da yawan samuwar ibadun da ke ƙara kusanta bayi ga Ubangijinsu, da azumin watan Ramadan ke zuwa da shi kamar yadda malamai suka saba faɗa, Hakazalika kuma a watan na zuwa da wata al’ada mai ɗimbin tarihi da ke ɗebe wa al’umma musamman na Arewacin Najeriya kewa.
Wannan al’adar ita ce ta tashe da ake fara d zarar watan azumi ya kai kwanaki 10.
DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin AlbashiMaza da mata na gudanar da wannan al’ada ta hanyar yin shigar kwaikwayo tare da ɓatar da kama, su ringa zagayawa gidaje da kwararo-kwararo ɗauke da ganga da kayan kaɗe-kaɗe suna bugawa suna waƙa.
Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan wannan daɗaɗɗiyar al’adar, don jin inda ta samo asali, tarihinta da kuma yadda ake gudanar da ita.
Domin sauke shirin, latsa nan