Alhaji Dangote, hamshakin attajirin nahiyar Afirka, ya ce sun hada kai da gwamnatin jihar ne wajen tabbatar da ganin an raba abincin ga mabukata a kowace jiha dake fadin Nijeriya.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf wanda ya jagoranci kaddamar da rabon tallafin abincin a matakin kasa na wannan shekara, ya ce aiwatar da wannan shiri ya nuna tsantsar halin nuna jinkai da kulawar Alhaji Aliko Dangote wajen kawar da yunwa da fatara a Nijeriya.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Comrade Aminu Abdulsalam Gwarzo ya wakilta, ya ce za a raba buhun shinkafar guda dubu 120, mai nauyin kilogram 10 a daukacin kananan hukumomi 44 dake fadin jihar Kano.

A jawabinta ga manema labarai, Babbar Darakta kuma Babbar jami’ar gudanarwar gidauniyar Aliko Dangote, Zouera Youssoufou ta ce an tsara shirin ne a matsayin wata hanya ta tallafa wa gwamnatoci wajen yaki da talauci da yunwa a Nijeriya.

Mukaddashin Babban Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Dr. Mujahid Aminudden ya gode wa gidauniyar ta Dangote kan bijiro da wannan shiri, inda ya roki sauran ‘yan Nijeriya da suyi koyi da halin Dangote.

Ya ce Hukumar Hisbah za ta tsaya tsayin daka wajen ganin tallafin yaje hannun wadanda suka cancanta.

Wani da ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin mai suna Ibrahim Ahmed ya yaba wa Aliko Dangote, inda ya yi addu’ar Allah ya ci gaba da taimakonsa a harkokinsa na kasuwanci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Talakawa

এছাড়াও পড়ুন:

ECOWAS ta kaddamar da rundunarta mai dakaru 5,000 don yakar ta’addanci

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta kaddamar da wata rundinarta mai manufar yaki da ayyukan ta’addanci da miyagun laifuffuka a yankin.

Ministan tsaron Nijeriya, Mohammed Badaru Abubakar ne ya sanar da hakan a yayin taron Kolin ECOWAS na hafsoshin tsaro karo na 43 a babban birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Talata.

Badaru ya ce taron ya jaddada kudurinsu na magance matsalolin tsaro da ke addabar yankin.

 “Kaddamar da wannan runduna yana kara jaddada kudurinmu na tunkarar ta’addancin da ya shafi tsaron yankin,’’ in ji shi.

Taron ya samu halartar manyan hafsan hafsoshin tsaro na kasashen kungiyar ECOWAS, banda kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar wadanda suka raba gari da kungiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500
  • Ƙasar Sin Ta Yi Alƙawarin Ƙarfafa Hulɗar Da Ke Tsakaninta Da Kano
  • Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Karfafa Huldar Dake Tsakaninta Da Kano
  • Fiye Da Yara Mata 74,000 Sun Amfana Da Shirin Tallafin Kudi Na AGILE A Kano
  • Uwargidan Tinubu Ta Bai Wa Mata Manoma Tallafin Naira Miliyan 26 A Nasarawa
  • Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
  • ECOWAS ta kaddamar da rundunarta mai dakaru 5,000 don yakar ta’addanci
  • Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa  Tehran
  • Zulum ya bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin 1bn a Borno