Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi
Published: 14th, March 2025 GMT
Jihohin Sakkwato da Kebbi na fuskantar ƙalubale sakamakon cutar sanƙarau da ta ɓulla a jihohin, inda rahotanni suka tabbatar da cewa cutar ta kashe aƙalla mutum 50, yayin da sama da mutum 200 suka kamu da cutar.
A Jihar Kebbi, ƙananan hukumomin Aliero, Jega, da Gwandu ne suka fi fuskantar matsalar, inda cutar ta fara yaɗuwa kafin a ɗauki matakan gaggawa.
A Jihar Sakkwato kuwa, ƙaramar hukumar Tambuwal ce ta fi fama da cutar, lamarin da ya sa hukumomin lafiya suka sanar da ɗaukar matakan daƙile cutar domin hana ta yaɗuwa zuwa sauran yankunan.
Dalilin Yawaitar CutarMasana kiwon lafiya sun danganta yawaitar cutar da tsananin zafi da ake fama da shi a yankin Arewa Maso Yamma, wanda ke haifar da bushewar iska da kuma saurin bazuwar ƙwayoyin cutar sanƙarau.
Rashin isassun matakan rigakafi da kuma ƙarancin kula da lafiyar jama’a a wasu yankuna na daga cikin dalilan da suka sa cutar ke bazuwa cikin sauri.
Matakan da Aka ƊaukaGwamnatocin jihohin Kebbi da Sakkwato sun ce sun fara ɗaukar matakan gaggawa, inda ake gudanar da allurar rigakafi domin daƙile cutar, musamman ga ƙananan yara da tsofaffi, waɗanda suka fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar.
Hakazalika, an ƙara wayar da kan jama’a kan alamomin cutar da matakan kariya, domin daƙile yaɗuwarta a cikin al’umma.
Abubuwan da Jama’a Ke BuƙataDuk da matakan da hukumomi ke ɗauka, har yanzu jama’a na buƙatar ƙarin taimako, musamman wajen samun ingantattun cibiyoyin lafiya da isassun magunguna.
Akwai buƙatar gaggauta aika ƙarin kayayyakin kula da lafiya da ƙarfafa rigakafi domin hana aukuwar cutar a nan gaba.
A halin yanzu, hukumomin lafiya na ci gaba da sa ido kan lamarin, tare da jan hankalin jama’a da su guje wa cunkoso da kuma kai marasa lafiya asibiti da wuri idan suka fara ganin alamomin cutar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lafiya Sakkwato Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.
Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.
A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.
Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.
Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoA sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.
Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”
Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.