Aminiya:
2025-03-14@17:13:21 GMT

Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar

Published: 14th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta kafa sansanin soji a Ƙaramar Hukumar Arewa domin inganta tsaro.

Ya yi wannan roƙo ne bayan ziyarar da ya kai sansanin ‘yan gudun hijira a Kangiwa, bayan harin da wasu da ake zargin Lakurawa ne suka kai musu.

Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

Harin da aka kai a ranar 9 ga watan Maris ya yi sanadin mutuwar mutum 11 tare da ƙone ƙauyuka bakwai.

Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Birnin Debi, Garin Nagoro, da Garin Rugga.

“Sansanin soji a yankin zai taimaka wajen gaggauta kai ɗauki idan an kai wani hari,” in ji Gwamna Idris.

“Dole mu yi duk abin da za mu iya don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.”

Yayin ziyarar tasa, gwamnan ya yi alƙawarin taimakawa wajen sake gina gidajen mutanen da suka rasa matsugunansu.

Haka kuma, ya umarci hukumomin ƙaramar hukumar da su riƙa samar wa ’yan gudun hijirar abinci, tare da yanka saniya bayan kwana huɗu.

Bugu da ƙari, ya umarci a yanka raguna biyu don jarirai huɗu da aka haifa a sansanin yayin rikicin.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Alhaji Sani Aliyu, ya gode wa gwamnan bisa ƙoƙarin da yake yi.

“Gwamnatin jiha tana bakin ƙoƙarinta wajen magance matsalar tsaro, amma muna buƙatar ƙarin tallafi daga Gwamnatin Tarayya,” in ji shi.

Gwamnan ya buƙaci mutanen da abin ya shafa da su ci gaba da haƙuri da addu’a, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnati na ƙoƙarin kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamna Lakurawa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya yi ganawar sirri da gwamnan Bauchi

Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, ya yi ganawar sirri da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed.

Taron ya gudana ne a Ramat House da ke Bauchi, sai dai ba a bayyana manufar taron ba.

Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-Rufai ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja

Obi ya isa Filin Jirgin Sama na Abubakar Tafawa Balewa da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Alhamis, inda Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya tarbe shi.

Rahotanni sun nuna cewa Obi da Gwamna Mohammed sun tattauna wasu batutuwa da suka shafi babban zaɓen 2027 da kuma makomar siyasarsu.

Wannan ganawa ta wakana ne a daidai lokacin da ’yan siyasa ke shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.

Obi ya zo na uku a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, wanda tsohon gwamnan Jihar Legas, Bola Tinubu na jam’iyyar APC, ya lashe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kebe Filin Gina Hedikwatar NWDC
  • Peter Obi ya yi ganawar sirri da gwamnan Bauchi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
  • Za a mayar da waɗanda Lakurawa suka raba da garuruwansu – Gwamnan Kebbi
  • Majalisar Dattawa Ta Buƙaci A Kafa Sansanin Soji a Jihar Binuwai
  • Gwamnan Zamfara Ya Haɗa Kai Da Kamfanonin Sin Don Habaka Tsaro
  • An Bada Umarnin Sake Tsugunar Da Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Rutsa Da Su A Kebbi
  • Gwamnatin Zamfara Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Wajen Inganta Noma, Sufuri Da Ma’adanai 
  • Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike