Aminiya:
2025-04-14@16:41:25 GMT

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo

Published: 14th, March 2025 GMT

Wani direban motar bas ya murƙushe wata yarinya ’yar shekara biyu a ƙoƙarin gujewa kamun jami’an hukumar kare haƙƙin jama’a na Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a kan titin Ring Road da ke birnin Benin a ranar Laraba lokacin da jami’an hukumar suka yi artabu da wani direban motar bas a lokacin da suke ƙoƙarin kama shi.

Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar Mun ceto Najeriya daga faɗa wa mummunan yanayi — Tinubu

Shaidu sun ce lamarin ya ta’azzara ne a lokacin da jami’an da ke aikin suka tunkari direban inda yake ƙoƙarin tserewa ya sauya hanyar motar, amma jami’an sun kama sitiyarin motar.

“Motar ta murƙushe wata yarinya da ke tsaye kusa da kayayyakin mahaifiyarta, yayin da mahaifiyarta ta tsira da ƙyar,” in ji wani ganau.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Edo, Moses Yamu ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an fara bincike.

“Wata farar motar bas ƙirar Vannette mai lamba BEN 406 YA ta afka kan masu tafiya a ƙasa a lokacin da take ƙoƙarin gujewa kamawar jami’an tsaron. Abin takaici, wata yarinya ’yar shekara biyu ta rasa ranta, yayin da mahaifiyarta ke jinya a asibiti a halin yanzu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, jami’in tsaron da ake zargi da haddasa haɗarin tare da direban a yanzu haka suna hannun ’yan sanda domin gudanar da bincike.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hadarin mota

এছাড়াও পড়ুন:

Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar

Labaran da suke fitowa daga kasar Ukraine sun bayyana cewa, gwamnatin kasar tana son karban iko da bututun iskar gas na kasar Rasha wanda yake yammacin kasar da Turai, wanda kuma yake kai iskar gasa zuwa kasashen Turai.

An gina bututun tun zamanin tarayyar Soviet kuma kasashen biyu suna samun kudade masu yawa daga wannan bututun.

Gwamnatin kasar Amurka dai tana son ta dawo da kudaden da ta kashewa kasar Ukraine na makamai wacce ta karba a likacin shugaban Biden. Daga cikin dai Amurka ta bukaci Ukraine ta bada ma’adinanta na kimani dalar Amurka biliyon $500.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an gwanatocin kasashen Amurka da Ukraine sun tattauna wannan batun a ranar jumma’an da ta gabata, don tattauna batun irin ma’adinan da kasar Ukraine zasu bawa Amurka saboda biyan kudaden da take binta basgi. Har’ila yau Amurkawan sun gabatar da shawarar kasashen biyu su hada giwa don samun riba tare a aikin hakar Ma’adinan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi