Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo
Published: 14th, March 2025 GMT
Wani direban motar bas ya murƙushe wata yarinya ’yar shekara biyu a ƙoƙarin gujewa kamun jami’an hukumar kare haƙƙin jama’a na Jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a kan titin Ring Road da ke birnin Benin a ranar Laraba lokacin da jami’an hukumar suka yi artabu da wani direban motar bas a lokacin da suke ƙoƙarin kama shi.
Shaidu sun ce lamarin ya ta’azzara ne a lokacin da jami’an da ke aikin suka tunkari direban inda yake ƙoƙarin tserewa ya sauya hanyar motar, amma jami’an sun kama sitiyarin motar.
“Motar ta murƙushe wata yarinya da ke tsaye kusa da kayayyakin mahaifiyarta, yayin da mahaifiyarta ta tsira da ƙyar,” in ji wani ganau.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Edo, Moses Yamu ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an fara bincike.
“Wata farar motar bas ƙirar Vannette mai lamba BEN 406 YA ta afka kan masu tafiya a ƙasa a lokacin da take ƙoƙarin gujewa kamawar jami’an tsaron. Abin takaici, wata yarinya ’yar shekara biyu ta rasa ranta, yayin da mahaifiyarta ke jinya a asibiti a halin yanzu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, jami’in tsaron da ake zargi da haddasa haɗarin tare da direban a yanzu haka suna hannun ’yan sanda domin gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hadarin mota
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Iran ba za ta fara yaki ba amma za ta mayar da martani ga duk wata barazana
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya yi gargadin cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta taba neman wata kasa da yaki ba, amma kuma a lokaci guda ta shirya tsaf domin mayar da mummunan martani ga duk wata barazana ko shishigi daga makiya.
Janar Hossein Salami ya bayyana hakan ne a wannan Lahadi, bayan da Washington ta zargi Tehran da taimakawa sojojin Yaman a hare-haren da suka rika kaiwa haramtacciyar kasar Isra’ila a baya-bayan nan tare da yin kira da ta daina yin wanann zargi maras tushe balantana makama.
Salami ya ce, “Iran ba za ta taba zama mai fara yaki ba, amma idan aka fuskanci barazana, za ta mayar da martani mai tsanani.”
Shugaban kasar Amurka ya sake alakanta ayyukan da kungiyar Ansarullah ta Yaman ga Iran, ya kuma ce dole ne Iran ta daina goyon bayan kungiyar mai gwagwarmaya.”
Salami ya jaddada cewa, mutanen Yemen al’umma ce mai ‘yanci da ke bin manufofi na kashin kansu ba tare da an yi musu katsalandan ba. In ji babban kwamandan na IRGC.
Salami ya jaddada cewa, “Mu ba al’ummar da ke gudanar da ayyukanta cikin sirri ba ne; a maimakon haka, muna yin komai a bisa doka da oda da kuma kiyaye ka’idoji na duniya, kuma komai namua fili yake, kuma lokacin da muka dauki matakin soji a kan Isra’ila ba mu boye ma kowa ba kamar yadda duniya ta sheda hakan a cewar janar Salami.