Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo
Published: 14th, March 2025 GMT
Wani direban motar bas ya murƙushe wata yarinya ’yar shekara biyu a ƙoƙarin gujewa kamun jami’an hukumar kare haƙƙin jama’a na Jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a kan titin Ring Road da ke birnin Benin a ranar Laraba lokacin da jami’an hukumar suka yi artabu da wani direban motar bas a lokacin da suke ƙoƙarin kama shi.
Shaidu sun ce lamarin ya ta’azzara ne a lokacin da jami’an da ke aikin suka tunkari direban inda yake ƙoƙarin tserewa ya sauya hanyar motar, amma jami’an sun kama sitiyarin motar.
“Motar ta murƙushe wata yarinya da ke tsaye kusa da kayayyakin mahaifiyarta, yayin da mahaifiyarta ta tsira da ƙyar,” in ji wani ganau.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Edo, Moses Yamu ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce an fara bincike.
“Wata farar motar bas ƙirar Vannette mai lamba BEN 406 YA ta afka kan masu tafiya a ƙasa a lokacin da take ƙoƙarin gujewa kamawar jami’an tsaron. Abin takaici, wata yarinya ’yar shekara biyu ta rasa ranta, yayin da mahaifiyarta ke jinya a asibiti a halin yanzu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, jami’in tsaron da ake zargi da haddasa haɗarin tare da direban a yanzu haka suna hannun ’yan sanda domin gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hadarin mota
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kulla haɗin gwiwa mai muhimmanci da Jami’ar Azman domin faɗaɗa damar ilimi da inganta ci gaban al’ummar jihar.
An bayyana hakan ne lokacin da shugabannin Jami’ar Azman, karkashin jagorancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Fatima Batul Mukhtar, suka kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Wannan haɗin gwiwa yana da nufin tallafawa sabbin hanyoyin koyarwa, da daukar nauyin dalibai a wasu shirye-shirye na musamman, da kuma inganta basirar matasa a muhimman fannoni kamar lissafi da kwamfuta, da kimiyyar bayanai, da sarrafa harkokin jiragen sama, da sauransu.
Yayin da take jawabi, Shugabar Jami’ar ta nuna godiya ga jajircewar gwamnatin jihar wajen bunkasa ilimi, tare da jaddada aniyar jami’ar wajen samar da inganci da kirkire-kirkire.
Ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta hada kai da jami’ar wajen shirye-shiryen horar da matasa da ba su takardun shaidar ƙwarewa, musamman a bangaren shirye-shiryen kwamfuta, tare da manyan kamfanoni irin su Cisco, Huawei, da Oracle Academy.
“Mai Girma Gwamna, Jami’ar Azman ta riga ta samu ci gaba a shirye-shiryen kwamfuta, domin mun yi rijista da Cisco, Huawei, da Oracle Academy, kuma muna da malamai da ke da takardar shaidar koyarwa daga Huawei. Saboda haka, muna rokon ku da ku duba yiwuwar yin haɗin gwiwa da mu a shirye-shiryen takardun shaidar ƙwarewa a bangaren shirye-shiryen kwamfuta.”
Shugabar Jami’ar ta kuma yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta a fannin ilimi, musamman ware kaso 32 bisa dari na kasafin kudin 2024 ga bangaren ilimi da kuma ƙarin naira biliyan uku da aka ƙara wa Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Jigawa.
A nasa martanin, Gwamna Namadi ya nuna matuƙar godiya ga ƙoƙarin Jami’ar Azman tare da yabawa shugabancin Farfesa Fatima Batul Mukhtar.
Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin shirye-shiryen musamman da jami’ar ke bayarwa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana da shirin daukar nauyin wasu dalibanta domin su yi karantu a bangarorin da babu a sauran makarantu a jihar.
“Sabbin kwasa-kwasan da kuka kirkiro suna da kyau, kuma hakan zai jawo hankalin dalibai da malamai zuwa jami’ar.
Wannan na daga cikin dalilan da suka sa na ga babbar dama a wannan jami’a. Kwasa-kwasan da kuka ambata suna da matukar muhimmanci, musamman a yankunan da basu dawannan taarin karatu.”
Usman Muhammad Zaria