Gwamnatin Jigawa Da Bankin Duniya Sun Dauki Nauyin Dalibai 500 A Fannin Fasahar Zamani
Published: 14th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, ta dauki nauyin dalibai sama da 500 a wani mataki na tsara makomar matasa a fannin fasahar zamani.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin bikin kaddamar da shirin da kuma mika takardun shaidar karatu ga wadanda suka ci gajiyar shirin fasahar zamani na Innovation Development and Effectiveness in the Acquisition of Skills (IDEAS) a Jihar Jigawa.
Malam Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na karfafawa matasa ta hanyar kirkire-kirkire a fannin fasahar zamani da kuma koyon sana’o’i don habaka tattalin arziki.
“A yau, mun kammala horar da dalibai 240 da suka koyi yadda za su bunkasa harkokinsu na kasuwanci don tabbatar da ci gaba mai dorewa,” in ji gwamnan.
“Haka kuma, a yau muna mika takardun shaidar karatu ga dalibai 550 da suka sami guraben karatu ta hannun Hukumar Samar da Ayyuka da Taimakon Matasan Jihar Jigawa, tare da hadin gwiwar Bankin Duniya, Arms of Ideas, da gwamnati.”
A cewarsa, wadannan dalibai da suka sami guraben karatu a Jami’ar Baze za a horas da su a fannonin fasahar zamani da ke taka muhimmiyar rawa a kasuwannin duniya.
Gwamna Namadi ya bayyana cewa karkashin wannan shiri, Gwamnatin Jihar Jigawa da Bankin Duniya sun saka hannun jarin sama da Naira miliyan 100 domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi da koyon sana’o’i.
“Wannan kudade hadin gwiwa ne tsakanin Bankin Duniya da Gwamnatin Jihar Jigawa. Bankin Duniya ya bayar da Naira miliyan 85, yayin da gwamnatin jihar ta bayar da Naira miliyan 50, kuma an riga an biya kudaden gaba daya.”
Ya kara da bayanin cewa shirin zai ba dalibai damar koyon akin binciken sirri, (Artificial Intelligence), da fasahar blockchain, binciken kasuwanci (Business Intelligence), da tsaron yanar gizo (Cybersecurity), da sauransu.
Baya ga horon fasahar zamani, gwamnan ya kuma sanar da kammala horas da matasa ‘yan kasuwa 240 da suka samu horo kan hanyoyin bunkasa kasuwancinsu. Ya kara da cewa kowannensu zai samu tallafin jari na Naira 50,000 domin fadada kasuwancinsu da kuma tabbatar da dorewarsa.
Saboda haka, Gwamna Namadi ya bukaci daliban da su yi amfani da wannan dama yadda ya kamata, tare da tabbatar musu da karin tallafi ga wadanda suka yi fice a karatunsu.
“Ina bukatar ku yi kokari don cimma wannan buri. Duk wani dalibi da ya kammala karatu da Upper Credit ko Distinction zai samu sabuwar kwamfutar tafi-da-gidanka (laptop) domin tallafa masa!”
Ya sake tabbatar da goyon bayan gwamnatinsa ga fannin fasahar zamani, da karfafawa matasa tattalin arziki a Jihar Jigawa, tare da alkawarin gabatar da karin manufofi da shirye-shirye don inganta rayuwarsu da kuma bunkasa sana’o’insu.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bankin Duniya Jigawa Gwamnatin Jihar fasahar zamani Bankin Duniya Jihar Jigawa tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Kano Ta Kebe Filin Gina Hedikwatar NWDC
Hukumar raya yankin arewa maso yamma NWDC ta bukaci gwamnatocin jihar Kano da su taimaka tare da hadin gwiwa da nufin cimma manufofinta.
Shugaban Hukumar Alhaji Isma’il Lawal Abdullahi Yakawada ya nemi hadin kan a lokacin da ya jagoranci mambobin hukumar a ziyarar ban girma da suka kai wa gwamnan a gidan gwamnatin Kano.
Ya ce hukumar ta NWDC na da burin tabbatar da ci gaba da bunkasar jihohin Arewa maso Yamma, tare da mai da hankali wajen magance matsalolin da suka addabi kasa kamar rashin tsaro, yunwa, fatara, da rashin abinci mai gina jiki.
Ya nemi goyon bayan da ake bukata da hadin gwiwar gwamnatin jihar Kano domin cimma aikin da ke gabansa.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu kan kafa hukumar NWDC, inda ya yaba da matakin sanya hedikwatar hukumar a Kano ba tare da la’akari da harkokin siyasa ba.
Gwamnan ya jaddada aniyar gwamnatin jihar Kano na tallafawa manufofin hukumar, tare da amincewa da kafa hukumar ta NWDC a kan lokaci domin tunkarar kalubalen da yankin ke fuskanta.
“Mun riga mun samar da filin da ya dace wanda zai yi aiki don gina ofisoshin wannan hukuma mai daraja.”
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da cewa, yankin Arewa maso Yamma na fuskantar kalubale da suka hada da rashin tsaro, garkuwa da mutane, fashi da makami, da sauran ayyukan muggan laifuka.
” Ana sa ran kafa hukumar ta NWDC zai taimaka wajen magance wadannan al’amura, da inganta ci gaban tattalin arziki, hadin kan al’umma, da inganta rayuwar jama’a.”
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO