Alhaji Aminu Babba Ɗan Agundi (Sarkin Dawaki Babba) bai gamsu da wannan hukunci ba, don haka ya shigar da ƙara yana neman a dakatar da aiwatar da hukuncin har sai Kotun Ƙoli ta yanke hukunci.

Ya shigar da Gwamnatin Jihar Kano, Kakakin Majalisar Dokokin Jiha, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Hukumar NSCDC, da sauran hukumomin tsaro ƙara.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta amince da buƙatar Dan Agundi, inda ta ce akwai hurumin shari’a a cikin ƙarar.

Mai shari’a Abang ya bayyana cewa kotu dole ne ta yi adalci wajen yanke hukunci.

Wannan hukunci yana nufin cewa dole ne dukkan ɓangarorin su ci gaba da zama yadda suke kafin Babbar Kotun Tarayya ta yanke hukunci.

Bugu da ƙari, kotu ta umarci Dan Agundi da ya bayar da tabbacin shari’a cikin kwanaki 14, inda zai ɗauki alhakin duk wata asarar da za ta iya tasowa idan aka samu cewa dakatarwar ba ta da amfani a nan gaba.

Har yanzu rikicin masarautar Kano bai ƙare ba, kuma ana jiran Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na ƙarshe kan lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Rikicin Masarauta ta yanke hukunci

এছাড়াও পড়ুন:

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur 

Wata sanarwa da Ma’aikatar Kuɗi ta fitar ta ce: “Wannan tsari ba na wucin gadi ba ne. Tsarin sayar da ɗanyen mai a farashin Naira wata dabara ce ta bunƙasa tace mai a cikin gida da kuma bunƙasa tsaron makamashi a Nijeriya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci
  • Har Yanzu Shugabanci NNPP Na Hannunmu – Tsagin Kwankwaso
  • Masarautar Kauru Ta Bayyana Rashin Sha’awarta Kan Shiga Sabuwar Jihar Gurara
  • Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo
  • Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
  • Sudan Ta Kai Karar HDL A Gaban Kotun Kasa Da Kasa Ta MDD
  • Sudan ta kai karar Hadaddiyar Daular Larabawa a Kotun ICJ
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur 
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China