Aminiya:
2025-03-14@19:42:59 GMT

Wata mata ta faɗa ruwa ta mutu a Legas

Published: 14th, March 2025 GMT

An tabbatar da mutuwar wata mata da har yanzu ba a bayyana sunan ta ba bayan ta yi tsalle ta faɗa kogin Legas daga gadar Third Mainland a Jihar Legas.

Majiyar PUNCH ta ruwaito hakan ne daga wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Legas, Benjamin Hundeyin ya fitar a ranar Juma’a cewa lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 4 na yamma kusa da bakin ruwan kogin da ke hanyar jami’ar Legas.

Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Lakurawa: Gwamnan Kebbi ya nemi a kafa sansanin soji a jihar

“Tawagar ’yan sandan ruwa da ke aiki a wurin sun gano ta gaɓar ruwan da ke hanyar jami’ar Legas kuma likitocin jami’ar UNILAG sun tabbatar da mutuwarta a gaban rundunar  ’yan sanda daga sashin Sabo,” kamar yadda sanarwar a wani ɓangare ta bayyana.

Hundeyin ya ci gaba da cewa, an kai gawar zuwa ɗakin ajiye gawarwaki na Asibitin cututtuka masu yaɗuwa da ke yankin Yaba a jihar domin adanawa.

Ya ƙara da cewa “Yan sanda a halin yanzu suna binciken al’amuran da suka shafi mutuwar matar.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka

Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin da Amurka ta kakabawa Ministan Man Fetur na aksar Mohsen Paknejad da wasu hukumomi da jiragen ruwa masu ruwa da tsaki a harkar danyen man fetur da kasar ke fitarwa, tana mai cewa matakin keta doka da munafunci ne daga bangaren Amurka.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baghaei ne ya bayyana hakan yau Juma’a, kwana guda bayan da ma’aikatar baitul malin Amurka ta kakaba takunkumi kan ministan man fetur na kasar Paknejad da wasu kamfanoni uku da ke da hannu a cinikin man Iran a kasar Sin.

Mista Baghaei ya ce, sabbin takunkumin sun karyata ikirarin da jami’an Amurka suke yi kan aniyarsu ta yin shawarwari tare da Iran.

Ya kara da cewa, munanan ayyukan da Amurka ta yi da nufin kawo cikas ga mu’amalar tattalin arziki da cinikayya da Iran da sauran kasashen duniya, ya zama keta dokokin kasa da kasa da cinikayya cikin ‘yanci.

Kakakin ya kara da cewa, matakin da Amurka ta dauka na na sanya wa ministan man fetur na kasar takunkumi, ba zai iya yin wani tasiri ga kudurin kasa na kare ‘yancin kai da martabar kasar da kuma kokarin samar da ci gabanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo
  • Sama da ‘Yan Mata 74,000 Suka Amfana Shirin AGILE Cash A Kano
  • Mun ceto Najeriya daga faɗa wa mummunan yanayi — Tinubu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
  • Fiye Da Yara Mata 74,000 Sun Amfana Da Shirin Tallafin Kudi Na AGILE A Kano
  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina
  • HOTUNA: Fashewar tankar gas ta kashe gomman mutane a Legas
  • EU ta jadadda bukatar warware batun Iran ta hanyar diflomasiyya