MDD : Kwamitin Sulhu ya yi tir da kisan kiyashin Siriya
Published: 14th, March 2025 GMT
Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ya yi Allah wadai da kisan kiyashin da aka yi a baya-bayan nan a yammacin Syria, inda ya yi kira ga hukumomin rikon kwarya a kasar, da su kare “dukkan ‘yan Syria ba tare da nuna bambanci ba,” ba tare da la’akari da kabila, addini ba.
Majalisar ta yi kakkausar suka kan tashe-tashen hankulan da ke faruwa a lardunan Latakia da Tartus tun daga ranar 6 ga Maris, ciki har da kisan kiyashin da aka yi wa fararen hula, musamman a cikin al’ummar Alawite, ‘yan tsirarun da ke da alaka da dangin tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
Shugaban hukumar yan gudun hijira na MDD Filippo Grandi wanda ya ziyarce sansanonin yan gudun hijira na kasar Sudan a Chadi ya bayyana cewa akwai bukatar kasashen duniya su taimaka don kula da bukatun yan kasar sudan wadanda suke gudun hijira a kasar Chadi.
Grandi ya kara da cewa akwai bukatar agaji da gaggawa zuwa kasar Chadin da kuma sauran kasashen da suke daukar nauyin yan gudun hijira na sudan. A halin yanzu dai ana ganin mutane kimani 20,000 ne suka rasa rayukansu, sannan wasu da dama suka ji rauni sannan wasu kuma suka zama yan gudun hijira.