Jami’in Sin: Ba Za A Lamunci Ayyukan ‘Yan Aware Na “Ballewar Taiwan” Ta Ko Wace Hanya Ba
Published: 15th, March 2025 GMT
Wani jami’in yada labarai na babban yankin kasar Sin ya bayyana a jiya Alhamis cewa, ba za a amince da duk wani mahaluki ko wata runduna da za ta raba yankin Taiwan da kasar Sin ba, kuma babu yadda za a yi a lamunce da ayyukan “ballewar Taiwan” ta ko wace hanya.
Jami’in yada labarun, da ke aiki a ofishin kula da harkokin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin, Chen Binhua ya kara da cewa, matukar dakarun ‘yan awaren suka kuskura suka bari tura ta kai bango, za a dauki kwararan matakan mayar da martani a kansu.
Chen ya bayyana hakan ne a lokacin da yake yin tir da kalaman jagoran ‘yan awaren Taiwan na baya-bayan nan, Lai Ching-te, wanda ya yi ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin Taiwan ba su nuna biyayya ga junansu.
Da yake mayar da martani kan haka, Chen ya jaddada cewa, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin da ba za a iya rabuwa da shi ba. Kana bai taba zama kasa ba kuma ba zai zama ba a gaba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Tommy Bruce a cikin wata sanarwa da ya fitar ya bayyana cewa: Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun tattauna kan yunkurin diflomasiyya a Gaza na sakin mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma samar da tsagaita bude wuta mai dorewa a Gaza inda Hamas ta samu cikaken kwance damarar makamai da nakasassu.
An gudanar da taron ne a daidai lokacin da ake ci gaba da yin kiraye-kirayen a samar da mafita a siyasance a yakin Gaza, inda Isra’ila ta kashe Falasdinawa fararen hula fiye da 50,000 tun daga watan Oktoban 2023 (Bahan 1401).
A yayin da Amurka ke ci gaba da goyon bayan munanan hare-hare na gwamnatin sahyoniyawan da kuma kokarin shiga tsakani kan yarjejeniyar daidaita alaka tsakanin Saudiyya da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, Riyadh ta jaddada tsagaita bude wuta nan take a zirin Gaza da kuma hanyar samar da kasashe biyu.
A watan da ya gabata, shugaban Amurka Donald Trump ya ce watakila ya ziyarci Saudiyya tun a farkon wannan watan (Afrilu). A wa’adin farko na gwamnatin Trump a shekarar 2017, Saudiyya ita ce kasar farko da Trump ya fara zuwa kasashen waje. Duk da haka, Axios ya ruwaito cewa tafiya za ta faru a tsakiyar watan Mayu.
Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun kuma tattauna kan wasu batutuwan yankin da suka hada da yakin Sudan da Yemen.
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta ce: Ministocin harkokin wajen Amurka da na Saudiyya sun kuma amince da cewa, sojojin kasar Sudan da dakarun da ke ba da goyon baya cikin gaggawa su koma kan teburin sulhu, da kare fararen hula, da bude kofofin jin kai, da kuma komawa ga farar hula.