Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
Published: 15th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta ƙaryata zargin da Tsohon Gwamna Nasir El-Rufai ya yi cewa jami’an tsaro sun sace tsohon Kwamishinansa, Jafaru Sani.
El-Rufai ya yi wannan iƙirari ne a shafinsa na sada zumunta cewa an ɗauke tsohon Kwamishinan kamar fursuna ba tare da bin ƙa’idojin doka ba.
Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da KebbiYa yi zargin cewa wata “ƙungiyar masu garkuwa da mutane” da ke da alaƙa da Gwamna Uba Sani ce ke da alhakin ɗauke tsohon Kwamishinan.
Da yake mayar da martani, kakakin ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, ya bayyana zargin a matsayin ƙarya.
“Babu wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane a cikin Rundunar ’Yan Sandan Najeriya.
“Mu hukuma ce da ke aiki bisa kundin tsarin mulki don tabbatar da doka da oda,” in ji shi.
Ya buƙaci ’yan siyasa su guji yaɗa labaran da ba su da tushe.
“Yi wa jami’an tsaro ƙarya na iya haifar da ruɗani da kuma rage martabarsu. Idan mutum yana da ƙorafi, ya bi hanyar shari’a maimakon yaɗa kalaman da za su tayar da fitina,” a cewarsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jafaru Sani Tsohon Kwamishina zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Pakistan Ta Zargi Kasashen Afghanistan Da India Da Hannu A Garkuwa Da Jirgin Kasa Na Sojoji
Gwamnatin kasar Pakistan ta ce da akwai hannuwan Afghanistan da kuma India a garkuwa da jirgin kasa na soja da aka yi a cikin kasar a ranar 13 ga watan Maris,wanda ya jefa mutanen kasar cikin damuwa akan batun tsaro.
Mahukuntan kasar ta Pakistan sun kuma ce; Binciken farko ya tabbatar da cewa wasu masu dauke da makamai ne su ka yi garkuwa da jirgin kasar, da sun shigo ne daga iyakar Pakistan sai kuma wani dan India wanda ya shiya yadda za a yi.
Gwamnatin kasar ta Pakistan ta sanar da tsananta matakan tsaro domin kame wadanda su ka yi garkuwa da jirgin da kuma daukar matakan hana, irin haka faruwa a nan gaba.
Ya zuwa yanzu babu wata kungiyar da ta fito fili ta dauki alhakin abinda ya faru.
Gwamnatin kasar ta Pakistan ta ce, da akwai masu dauke makamai da sun kai 50 da suke garkuwa da jirgin kasan. Ya zuwa yanzu dai mutane 31 ne su ka rasa rayukansu da usn kunshi jami’an tsaro da kuma fararen hula.
A cikin shekarun bayan nan alaka a tsakanin Pakistan da Afghanistan ta kara kamari.