Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump
Published: 15th, March 2025 GMT
Gwamnatin kasar Amurka ta ce bata bukatar samuwar jkadan kasar Afrika ta kudu Ebrahim Rasool a kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto sakataren harkokin wajen kasar Amurka Marco Rubio yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Jumma’a, ya kuma kara da cewa Rasool mutum ne wanda yake nuna wariya, yake kuma kin Amurkawa.
Rubio bai bayyana dalilan daukar wannan matakin a kan jakadan ba, amma hakan ya faru ne bayan da Jakadan Rasool ya wata cibiyar bincike na Afrika ta kudu inda a jawabin da ya gabatar ya zargi shugaban kasar Amurka Donal Trump da, da samar da shirin “sake maida Amurka kasa babba” da wani shirin fifita fararem Amurka a kan sauran mutane a duniya.
Labarin ya kara da cewa tun lokacinda Trump ya sake dawowa fadar white house aka hana jakadan Afirka ta kudu a kasar ganawa da jami’an fadar white House kamar yadda ya dace. Fakon haka Amurka ta yi barazanar dakatar da tallafin da take bawa kasar Afrika ta kudu saboda karar da ta shigar kan HKI wacce ta aiwatar da kissan kiyashi kan Falasdinawa a Gaza daga ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 har zuwa yanzun. Banda haka kasar ta sami goyon baya daga kasashen duniya da dama. Kuma gwamnatin Amurka ta bukata Afirka ta kudu ta janye karar amma taki amincewa.
Ya zuwa yanzu dai kotun ta ICC ta fidda sammacin kama Firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma tsohon ministansa na Tsaro Yauf Galant. Kafin haka dai Ebrahim Rasool ya taba zaman jakadan Afrika ta kudu a kasarAmurka daga shekara ta 2010-2015 a lokacin shugabancin Barak Obama
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Yaki Na HKI Yace Sojojin HKI Zasu Ci Gaba Da Zama A Kasar Siriya Har’abada
Minisyan yaki na HKI Israel Kazt ya bayyana cewa sojojin HKI za su ci gaba da zama a kasar Siriya har zuwa illa masha allah, don kare yahudawan da suke zaunwa a tuddan Golan na kasar Siriya da suka mamaye a yakin kwanaki 6 a shekara ta 1967.
Tashar talabijin ta Presstv TV ta nakalto ministan yakin ya na fadar haka a jiya Talata, a lokacinda ya kai ziyara kan ‘Jabal Sheikh’ wani tsauni mai muhimmanci a fagen tsaro, wanda sojojin HKI suka mamaye bayan faduwar gwamnatin Bashar Al-Asad da yan kwanaki. Da kuma bayan da Abu Mohammed al-Julani shuga kungiyar Deash ya shiga fadar gwamnati a Damascus.
Jabal sheikh dai yana da tsawo sosai ta yadda ana iya kallon dukkan yankunan da ke kusa da shi a cikin kasar Lebanonn da kuma cikin birnin Damascus babban birnin kasar ta Siriya.
Jabal Sheik dai yana tazarar kilomita 20 kacal daga fadar gwamnatin kasar ta Siriya.
Daga karshe yace sojojin Israila sun dawo kasar Siriya ne, ba ranar da zasu bar fice daga kasar.