Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada sanarwan cewa a shirye take da saki fursinonin HKI da Amurka, har ma da gawakin wasu 4, idan HKI ta dawo kan ci gaba da aiwatar da abubuwan da yarjeniyar tsagaita wuta a tsakaninta da HKI.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani Jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Jumma’a.

Ya kuma kara da cewa, wasu daga cikin wadanda suke tsakanin kungiyar da HKI ne ya bata wannan shawarar, sannan ya kara da cewa, sai dai wannan matakin yana da sharudda, kuma sune HKI ta amince ta dawo kan tattaunawa marhala ta biyu don aiwatar da yarjeniyar da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.

Taher al-Nounou ya fadawa kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa kan cewa Hamas zata salami Edan Alexander wanda yake dauke da passport na Amurka da kuma wasu 4 wadanda suke dauke da Passport na kasashen biyu wato HKI da kuma Amurka. Amma tare da wannan sharadin.

Sanarwan ta kammala da cewa kungiyar ta fara sabuwar tattaunawa a birnin Doha na kasar Qatar a ranar Talatan da ta gabata sannan tawagar HKI ma tana halattar tattaunawan wand aba kai tsaye ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ukraine Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Wata Guda Da Rasha

Majiyoyi sun bayyana cewa Donald Trump na shirin tattaunawa da Vladimir Putin a cikin makon nan domin ƙara fahimtar juna dangane da wannan shiri.

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, na kira ga ƙasashen Turai da su haɗa kai domin tallafa wa Ukraine wajen tabbatar da tsaron ƙasar bayan wannan tsagaita wuta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna
  • Ukraine Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Wata Guda Da Rasha
  • Za a Dawo da Wurin Sarrafa Iskan Shaka Oxygen nan Badadewa Ba – AKTH
  • FERMA Ta Sake Jaddada Sadaukarwar Da Take Yi Na Kula Da Hanyoyin Tarayya
  • Hamas ta yi maraba da matakin Yemen na haramtawa jiragen ruwan Isra’ila shiga teku
  • Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi