Jumhuriyar Najer Ta Bukaci Tarayyar Najeriya Ta Taimaka Don Warware Matsalar Karancin Makamashi A Kasar
Published: 15th, March 2025 GMT
Kimani makonni biyu Kenan jumhuriyar Najer tana fama da karancin man fetur a gidajen man kasar, wanda ya rage zirga-zirgan ababen hawa a duk fadin kasar har da Yemai babban birnin kasar, har’ila yau ya shafi harkokin tattalin arzikin kasar.
Shafin yana labarai na yanar gizo IR News, ya bayyana cewa bayan da gwamnatin sojojin kasar ta kasa magance matsalar a cikin gida, ta tura wata tawaga karkashin jagorancin Ministan man fetur na kasar zuwa tarayyar Najeriya tare da bukatar ta aiko mata tataccen man fetur don magance matsalar.
Labarin ya kara da cewa, gwamnatin tarayyar Najeriya dai tuni ta amince da bukatar, tare da bada umurnin a aikawa Jumhuriyar ta Niger tankunan man fetur har 300.
Wasu wadanda suka san al-amura a Jumhuriyar ta Niger sun bayyana cewa matsalar ta taso ne bayan da gwamnatin sojojin kasar suka sami matsala da kamfanin kasar China wanda yake haka da tashen man fetur a matatan mai ta Soraz, wanda ya kai da sojojin suka bukaci mutanen china su bar kasar.
JMI tana haka da sarrafa danyen man fetur tun shekara ta 2011, amma matsala tsakanin gwamnatin sojojin kasar da kasar China ta sa sun kasa samar da man da zai water da kasar, ballanta na a yi maganar ganga 100,000 da kasar take son fara saida shi ga kasashen waje, ta hanyar bututun mai wanda zai bi ta kasar Benin zuwa kasuwannin duniya.
Juye-juyen mulkin da aka yi a yankin Sahel dai ya sa Jumhuriyar Niger bata jituwa da kasashen kungiyar ECoWAW. Wacce Najeriya take jagoranta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin da Amurka ta kakabawa Ministan Man Fetur na aksar Mohsen Paknejad da wasu hukumomi da jiragen ruwa masu ruwa da tsaki a harkar danyen man fetur da kasar ke fitarwa, tana mai cewa matakin keta doka da munafunci ne daga bangaren Amurka.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baghaei ne ya bayyana hakan yau Juma’a, kwana guda bayan da ma’aikatar baitul malin Amurka ta kakaba takunkumi kan ministan man fetur na kasar Paknejad da wasu kamfanoni uku da ke da hannu a cinikin man Iran a kasar Sin.
Mista Baghaei ya ce, sabbin takunkumin sun karyata ikirarin da jami’an Amurka suke yi kan aniyarsu ta yin shawarwari tare da Iran.
Ya kara da cewa, munanan ayyukan da Amurka ta yi da nufin kawo cikas ga mu’amalar tattalin arziki da cinikayya da Iran da sauran kasashen duniya, ya zama keta dokokin kasa da kasa da cinikayya cikin ‘yanci.
Kakakin ya kara da cewa, matakin da Amurka ta dauka na na sanya wa ministan man fetur na kasar takunkumi, ba zai iya yin wani tasiri ga kudurin kasa na kare ‘yancin kai da martabar kasar da kuma kokarin samar da ci gabanta.