Aminiya:
2025-04-14@16:13:25 GMT

Zulum ya bai wa jami’an tsaro kyautar gidaje da motoci a Borno

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bai wa jami’an ‘yan sanda kyautar gidaje 280 tare da bayar da gudunmuwar motoci 110 da babura 500 domin inganta tsaro a jihar.

Wannan shiri na da nufin inganta jin daɗin jami’an tsaro da kuma ƙarfafa yaƙi da aikata laifuka da ta’addanci.

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

A wajen bikin rabon kayayyakin a Maiduguri, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, ya jinjina wa gwamna Zulum kan goyon bayansa ga jami’an tsaro.

Ya ce wannan tallafi mataki ne mai kyau wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Borno.

“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba wajen kula da jin daɗin jami’an da ke sadaukar da rayuwarsu don kare al’umma,” in ji Zulum.

“Waɗannan motoci za su taimaka wajen inganta zirga-zirga da hanzarta kai ɗauki a lokacin buƙata.”

Egbetokun ya bayyana wannan gudunmuwa a matsayin wani babban ci gaba.

“Wannan tallafi zai ƙarfafa gwiwa da inganta ayyukan jami’anmu,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma gode wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa jagorancinsa wajen tallafa wa jami’an tsaro.

Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da kayan aiki da duk wani abu da zai taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Manyan jami’an tsaro, ciki har da shugabannin ’yan sanda da sojoji, sun halarci taron, inda suka jaddada buƙatar haɗin gwiwa don tunkarar ƙalubalen tsaro a jihar.

Ga hotunan a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jami an Tsaro kyauta jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yanzu haka al’ummar Borno na cikin zullumi sakamakon wasu hare-haren da ake zargin ƙungiyar Boko Haram ce ta kai a wasu sassan jihar.

Waɗannan hare-hare dai suna faruwa ne bayan shekaru da dama da iƙirarin hwamnati cewa an yi nasarar nakasa ƙungiyar.

Ko mene ne dalilin sake farfaɗowar ƙungiyar ta Boko Haram a wannan lokaci?

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Wannan ne batun shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa https://www.buzzsprout.com/1822045/episodes/16971864-dalilan-farfa-owar-boko-haram-a-jihar-borno.mp3?download=true

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • ‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Mamaye Sassan Jihar Borno -Zulum
  • Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe