Leadership News Hausa:
2025-03-17@07:25:02 GMT

Majalisa Ta Bukaci CBN Ya Gaggauta Dakatar Da Karin Caji A ATM

Published: 15th, March 2025 GMT

Majalisa Ta Bukaci CBN Ya Gaggauta Dakatar Da Karin Caji A ATM

Ya kara da cewa bisa sashin 10.7 da aka sake nazarinsa a 2019, ya rage cajin daga N65 zuwa N35 kan kowace hada-hada.
Sai dai ya bayyana cewa za a biya Naira 100 ga duk wanda aka cire na Naira 20,000 ga kwastomomi daga wasu bankunan da ke yin mu’amala da ATM a harabar bankin.

Onobun ya jaddada cewa abokan hulda daga sauran bankunan da ke yin mu’amala da ATMs a wajen harabar bankin, manyan kantuna, kasuwanni, da sauran wuraren taruwar jama’a, za a rika biyan su Naira 100 da karin N500.

Majalisar a cikin kudurorin ta ta bukaci CBN da ya gaggauta dakatar da aiwatar da wannan manufa, har sai an yi huldar da ta dace da kwamitocin da suka dace kan harkokin banki, kudi, da cibiyoyin hada-hadar kudi.

Ta koka da cewa tuni ‘yan Nijeriya ke fama da matsalolin tattalin arziki da dama, da suka hada da hauhawar farashin kayayyaki, karin farashin man fetur, karin kudin wutar lantarki, da yawan kudaden banki da na hidima da ke rage yawan kudaden shiga da ake iya kashewa da kuma yin illa ga tattalin arzikin ‘yan kasa.

‘Yan majalisar sun ce aikin gwamnati ya hada da kare ‘yan kasa daga ayyukan cin hanci da rashawa da ka iya haifar da kara tabarbarewar tattalin arziki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’

Shugaban Kasa, Bola Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatinsa ke yi, tana yi ne da nufin gyara makomar yara masu tasowa.

 

Yayin da yake jawabi ga kungiyar ‘Yan majalisa ta uku – wadda ya kasance cikin a Jamhuriya ta uku – da suka kai masa ziyara a fadarsa, Shugaba Tinubu ya ce a baya kasar na kashe kudaden yaran kasar da ba a kai ga haihuwarsa ba.

 

“Shekara 50 da suka gabata, Najeriya na kashe kudaden yaran da ba a kai ga haihuwarsu ba, tare da mayar da hankali kan man fetur wajen samun kudin shiga. Ba a yi wani tsari na tallafa wa yaran da za a haifa a gaba ba,” kamar yadda ya ce.

 

Shugaban ya kuma bayyana tarin matsalolin da ya fuskanta a farkon mulkinsa, musamman fannin tattalin arzikin da rayuwar jama’a.

 

“Mun fuskanci tarin kalubale a lokacin da na karbi mulki. Inda ba mu dauki matakai ba da yanzu kasar ta talauce, kuma ai hakkinmu ne mu kare tattalin arzikinmu daga rugujewa”, in ji Shugaba Tinubu.

 

To amma shugaban ya ce a yanzu kwalliya ta fara biyan kudin sabulu dangane da sauye-sauyen da gwamatinsa ta fara ɓullo da su.

 

“Amma a yau bayan shimfida mai kyau da muka yi, mun smau nasarar magance matsalolin da suka tunkaro kasarmu, a yanzu canjin kudi ya daidaita, farashin abinci na ci gaba da sauka, musamman a lokacin Ramadan, da yardar Allah wahalar ta zo karshe”, a cewar shugaban kasa.

 

Bello Wakili/Abuja

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC ta kama Murja Kunya kan wulaƙanta takardun Naira
  • Tattalin Arzikin Ghana Ya Bunkasa Da Kashi 5.7 A Shekarar 2024
  • Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
  • Tsohon Firaministan Lebanon: Rashin Fahimta Da Shakku Daga Waje Ba Za Su Iya Dakatar Da Ci Gaban Kasar Sin Ba
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  • Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa
  • Majalisa Ta Umarci NCC Ta Rufe Dukkanin Shafukan Intanet Na Batsa A Nijeriya
  • ‘An Kwashe Shekaru Ana Kashe Kudaden Yaran da ba a ma Haife su ba a Nijeriya’
  • Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500