Shi ma, Manajan Darakta na CDI, Roland Oroh, ya goyi bayan wannan ra’ayi na Dakta Anyebe Idoga, inda ya sanar da cewa; wannan aiki, zai kara karfafa karfin Nijeriya wajen fitar da kaya zuwa ketare.

“Mun ji dadi kan fara wannan yarjejeniya da mu, domin wannan zuba hannun jari, zai taimaka wa Nijeriya wajen kara habaka fitar da ingantaccen nama zuwa ketare”, in ji Oroh.

Kazalika, an bijiro da wannan hadaka ce, sakamakon yadda Saudiyya ta nuna sha’awarta, na son shigar da nama zuwa kasarta daga Nijeriya, wanda ya kai tan 176,000 a duk shekara, tare da kuma ciyawar dabbobi ta alfalfa hay da abincin dabbobi da ake sarrafawa da kuma Waken Soya.

A yanzu haka, CDI na ci gaba da tattaunawa da SALIC, musamman domin cimma bukatar samar da naman, wanda hakan zai kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

Wannan hadaka a tsakanin sauran sassan gwamnati daban-daban da CDI ke jagoranta, manufar ita ce; domin fitar da nama ketare kimanin tan 35,200 zuwa karshen 2025.

Bugu da kari, masu ruwa da tsaki a sassan kula da ayyukan kula da dabbobi da kwararrun likitocin dabbobi, duk an sanya su a cikin wannan aiki.

Aikin mayankar na Jurassic, ya kai na dala miliyan 10; wanda kuma ake gudanar da shi a hekta 50 da ke Nasarawa Egon, cikin Jihar Nasarawa.

Ana sa ran, za a kammala wannan aikin a watan Satumban 2025, inda wajen aikin zai dauki yawan Shanun da za a yanka da suka kimanin 1,000 da kuma Akuyoyin da za a yanka a kullum.

Kazalika, aikin zai taimaka wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye, sama da 20,000 da kuma ayyukan yi wadanda ba na kai tsaye ba, kimanin 100,000 tare da kara bunka tattalin arzikin Nijeriya da kuma daga darajar Naira.
A shirin fitar da Naman, an kiyasta samar da kudin shiga da ya kai kimanin dala miliyan 273, wanda ya yi daidai da Naira biliyan 451 kafin zuwa 2025.

Wannan hadakar ta nuna irin kokarin da Nijeriya ke yi, duba da cewa; hakan zai kara wajen ganin ana amfana da fannin na aikin noman, tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Waraka Daga Bashin Ketare

 

Amfanuwa Da Mamakon Arziki Da A Ka Yi Mana Baiwarsu

Babu shakka, mutuwar zuciya ce ta mai da jama’ar wannan Kasa tamu ta Nijeriya dogara kacokan da sabgar man fetur, a matsayin wata hanya daya tilo da za ta rika samar mana da sama da kashi tamanin ga tattalin arzikinmu na Kasa!. Hakika akwai hanyoyin arzuka iri daban daban cikin wannan Kasa, wadanda ma suka kere fetur sau ninkin ba ninki wajen bunkasar sha’anin tattalin arziki, musamnan sabgar noma, wadda wasu Shekaru can baya, ita ce kashin bayan tattalin arzikin wannan Kasa. Kuma, tun daga wancan lokaci zuwa yau din, harkar noma ce kan gaban fetur, wajen samawa dubban jama’ar Kasa aiyukan-yi.

Yankin arewacin wannan Kasa ta Nijeriya, na daga wuraren da suka fi ko’ina a Duniya kyawon kasar noma. Yankin na arewa, ya fi ko’ina a yankin Afurka ta yamma (West Africa) yawan matattarar ruwa, ko a ce dam dam, wanda ake amfani da su wajen noman rani. Ga dandazon albarkar jama’a da Allah Ya ba mu, wadanda za su wadata wajen noma irin wadannan kyawawan kassai da aka yi mana baiwarsu. Bangaren noman ne ke samawa dubban jama’ar yankin aiyukan-yi sama da komai a ban Kasa, sai dai, shugabanni sun gaza shigowa bangaren na noma, don inganta shi ingantawa.

A Kasar Amurka, Kasar da shugabanni suka shiga harkar tallafar noma kan-jiki kan karfi, ta tabbata cewa, kudin shigar da lemon zaki “Orange” kawai ke samawa Kasar a Shekara, ya fi kudin shigar da gwamnatin Nijeriya ke samu a Shekara wajen man fetur!. Ita kanta Amurkar, ba za ta fada mana ni’imar albarkatun kasa ba, amma sai ga su sun fi mu amfanarsu. Me ya sa? Amsa, shugabanninsu da gaske ne suke, a yunkurinsu na inganta tattalin arzikin Kasar.

Iskar gas kawai da Allah Yai wa Nijeriya baiwarsa, zai iya daukar nauyin bai wa daukacin nahiyar Afurka da ke kunshe da Kasashe 52 ko 53 wajen sama musu wadatacciyar iskar gas. To Amma dan Nijeriya a yau, nawa ne yake shan litar gas? Da kuma mai karatu zai lalubi wasu Kasashe cikin Duniya da ko kama kafarmu ba su yi ba wajen mallakar iskar gas din, sai ya samu kuma sun fi mu shan gas din da arha!. Wadanne irin shugabanni muke da su ne? Eh mana, tun da sarrafawa da inganta harkar gas din, na hannunsu ne.

Misali mutum ya ce fetur, gas, rake, lemo da makamantansu, za a ga an ba mu albarkatun kasa na abubuwa daidai har sama dari biyu da hamsin (250) iri daban daban. Cikin wadannan albarkatun kasa akwai bishiyar Katako, wani masani ke cewa, da Nijeriya za ta inganta bishiyoyin Katako da take da su, su kadai, za su iya zama abin dogara kamar man fetur, kuma su rike Kasar. Wane shiri ne a kasa a yau da mutanen wannan Kasa za su ce sun ga gwamnati na yi, don inganta sabgar bishiyoyin Katakonta?

Mutum ya dauki gyada kawai, zai yi matukar mamakin irin tattalin arzikin da ke kunshe cikinta. Daga gyada, akwai sinadaran da ake yin sabulu, abin yin biskit, abin yin abincin dabbobi, abincin kifi, abincin kaji da sauransu. Ka da mai karatu ya mance da man girki da ake samu daga gyadar. Ko mai karatu ya san da cewa a na yin makarin inji daga matsanancin hucin zafi, wanda a turance ake kira da “engine gasket” da bawon gyadar? To amma a yau, wane hobasa ne na hakika ba na baka ba, da za a ce gwamnatocinmu na yi, don ganin mun amfana hakikar amfanuwa daga mamakon tattalin arziki da ke kunshe cikin gyada?

Cikin wata budaddiyar wasika da Dattijo, Alhaji Dattijo Adhama ya rubuta zuwa ga hukumomi masu gudanarwa da masu yin doka na arewacin wannan kasar, “An Open Letter To The Northan Edecutibes & Legislatures” a Watan Yulin Shekarar 2021 (July, 2021), da mutum zai duba shafi na biyar (P5) na wannan wasika, zai amfana da wata irin kididdiga da aka yi, wadda ta nuna irin biliyoyin kudaden da jihar Kano za ta iya samu a kullum daga man gyadar da za a sha a cikin jihar. Cikin kididdigar, an nuna cewa, jihar ta Kano na iya samun kudin shiga sama da naira biliyan saba’in da biyu (N72b) a kullum. Da sharadin, wancan bangare na masu zartarwa da masu doka sun shigo sun gama kai wajeguda, tare da datse shigowar man gyadar daga Kasashen ketare, ta hanyar yin doka a Majalisa.

A tsakanin garin Makoda da Dambatta, akwai wani nau’in yashi da Kasar China ke ta begen ganin ta sami kai wa ga tononsa, don sana’anta gilashi da shi. Duk cikar Kasar ta China, ba su da wani ma’adin yin gilashi sama da irin wannan yashi na tsakanin Dambatta da Makoda. Idan ban manta ba, wani lokaci can baya, ta hanyar Malam Gambo, shugaban ma’aikata “Staff Officer” na Kasuwar Sabon Gari, ya gabatar min da shugabancin masu harkar gilashi ta Kasuwar Kofar Ruwa, na wuce gaba zuwa kai kuka ga Sanatan yankin, Barau Jibril”, da zimmar ya wuce musu gaba wajen tono yashin, amma lamarin ya gagari kundila.

Ba sai Kano ba, muddin mai karatu dan Nijeriya ne, ba zai gaza tunanin wani ma’adin ko albarkar Kasa da Allah Ya hore musu a yankinsu ba. Babbar matsalar a yau ita ce, masu mulki ba su damu da hako ko amfanar da jama’ar Kasa daga irin wadancan amfanoni da Allah Yai mana baiwarsu ba. Sai ma aka wayigari, idan akwai wani ma’adani a waje, sai a sami wasu marasa kishin kasa su game baki da Turawa, a zo a haddasa mummunar fitinar da za ta kai ga kashe rayukan dubban jama’a a wajen. Bayan kowa ya yi kaura ya yi gudun tsira da ransa, sai wadancan marasa kishin kasa da bakin haure su dukufa kwasar wadancan ma’adanai, shin, me ke faruwa a Zamfara a yau?

Duk irin albarkatun kasa da aka yi wa wata Kasa baiwarsa a Duniya, muddin shugabanninta ba sa kishinta, to fa a banza, ba za su amfana ba. Kuma ba za a bar su su zauna lafiya ba.

Da shugabanni a Nijeriya za su karkata ga sabgar noma kadai, su zuba jari ciki, su samawa manoman taki da kasuwa, babu shakka da an fita daga wannan kagaggen talaucin da aka jefa jama’ar wannan Kasa ciki. Talaucin Kasar Nijeriya ba daga ne yake ba, tun da Allahn Ya ba da mafita.

 

Samar Da Gungun Masana Masu Kishin Kasa

Dole ne gwamnati ta yi zabarin manyan mutane masana gogaggu, wadanda lamarin Kasar ne ke kunshe cikin zukatansu sabanin muradansu na son zuciya. Hakika Allah Yai mana baiwar mutane hazikai masana, wadanda hatta sassan Kasashen Duniya ke daukarsu aikin dindindin da na kwantaragi, don inganta harkokin Kasashen nasu. Dole ne a lalube su, a saurari shawarwarinsu, a dabbaka abubuwan da za su gabatar a matsayin shawara ko a matsayin wani sharadin da wajibi ne binsa, wajen inganta harkokin tattalin arzikin namu, muddin a na son A’i ta fita daga rogo ba tare da ta karce jiki ba.

Lokacin da marigayi Umar Musa ‘yar’adua ya tasamma yin gyara game da sha’anin Zabe a Nijeriya, ya kafa wani babban Kwamiti ne a karkashin tsohon babban Joji na Kasa Uwaisu, da sauran masu kishin kasa, mutane irinsu Farfesa Attahiru Muhammad Jega, OFR, ai sanin kowane cewa, a karshe, laya ta yi kyawon rufi. Gwamnati ba ta yi wa kwamitin wani katsa-landan ba, sannan kuma ta tasamma dabbaka irin shawarwarin da wancan kwamitin ya gabatar mata. Bugu da kari, gwamnati ta dauko guda daga cikin ‘yan kwamitin, Jega, ta danka hukumar zaben Kasar kacokan a hannunsa, hakan ne ya jaza aiwatar da zabukan da ba a taba samun masu ingancinsu ba cikin tarihin Zabukan Kasar gabaninsu, wato Zabukan Shekarun 2011 da na 2015, kamar yadda masana da sauran masu sanya idanu na gida da waje suka fadi.

Ko da an kafa wani kwamiti na masana kuma masu kishin kasar, muddin za a yi musu katsa-landan cikin sabgar kwamitin, ko kuwa, shawarwarin da suka gabatar, a yi wurgi da su, to fa babu inda za a je, sai dai kawai a ci gaba ne da tsalle a wajeguda kamar yadda aka saba.

Duk kyawon wani kwamiti da sunan gyara tattalin arzikin Kasa da aka kafa, ko za a kafa ba bisa cikakkiyar cancanta ba, shi ma ba zai cimma komai ba mai alfanu, lamura za su ci gaba da wakana ne cikin yanayi na daben-kwalo.

Duk karatu da Dr Abel Guobadia da Professor Maurice Iwu ke da, ba su jagorantar Hukumar Zabe, INEC, ta Kasa da aka yi bisa wata manufa, a karshen lamarin, sun gudanar da wasu nau’ikan Zabuka ne gurbatattu, wadanda gabaninsu a Kasar, ba a taba cin karo da miyagun Zabukan irinsu ba!.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Sin Za Ta Kara Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar Zuwa 125%
  • Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta