Gwamnatin kasar Pakistan ta ce da akwai hannuwan Afghanistan da kuma India a  garkuwa da jirgin kasa na soja da aka yi a cikin kasar a ranar 13 ga watan Maris,wanda ya jefa mutanen kasar cikin damuwa akan batun tsaro.

Mahukuntan kasar ta Pakistan sun kuma ce; Binciken farko ya tabbatar da cewa wasu masu dauke da makamai ne su ka yi garkuwa da jirgin kasar,  da sun shigo ne daga iyakar Pakistan sai kuma wani dan India wanda ya shiya yadda za a yi.

Gwamnatin kasar ta Pakistan ta sanar da tsananta matakan tsaro domin kame wadanda su ka yi garkuwa da jirgin da kuma daukar matakan hana, irin haka faruwa a nan gaba.

Ya zuwa yanzu babu wata kungiyar da ta fito fili ta dauki alhakin abinda ya faru.

Gwamnatin kasar ta Pakistan ta ce, da akwai masu dauke makamai da sun kai 50 da suke garkuwa da jirgin kasan. Ya zuwa yanzu dai mutane 31 ne su ka rasa rayukansu da usn kunshi jami’an tsaro da kuma fararen hula.

A cikin shekarun bayan nan alaka a tsakanin Pakistan da Afghanistan ta kara kamari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: garkuwa da jirgin

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar

Kwamandan sojojin kasa na JMI Laftanar-Janar Kiyomars Haydari ya bada sanarwan cewa; A bisa umranin jagoran juyin musulunci Imam Sayyid Ali Khamnei , sojojin kasa na JMI suna cikin shirin ko ta kwana domin mayar da martani akan kowace irin barazana ga tsaron kasar.

Laftanar janar Haidari ya kuma ce: A halin yanzu da akwai rundunoni 11 da su ke cikin shiri a kan iyakoki kasar domin sanya idanu da tattara bayanai saboda tabbatar da tsaron kasar.

Kwamandan sojan kasa na Iran ya kuma ce; Saboda sojojin suna cikin shirin ko-ta-kwana ne, barazanar da ake fuskanta ta zagwanye, da hakan ya ke a matsayin kandagarko.

Har’ila yau Laftanar janar Haidari ya yi ishara da rawar dajin da sojojin kasa su ka yi, har sau uku a cikin shekarar hijira Shamshiyya ta 1403. Sannan da wadanda za su a sabuwar shekara da za ta shigo.

Ya ce za’a gudanar da wani atisayen wanda zai da ce da girman barazanar da ake fuskanta.

Haidari ya kammala da cewa a sabuwar shekarar Iran da za a shiga, za ta zama ta kara yawan karfin tsaron kasar ne, domin takawa makiya birki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
  • Taron Kasashen Iran, Rasha Da China A Birnin Beijing Ya Bukaci A Kawo Karshen Takunkumai Akan Tehran
  • Sojojin Iran Sun Ce A Shirye Suke Su Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana Ga Tsaron Kasar
  • Iran da Belarus sun rattaba hannu kan daftarin bunkasa hadin gwiwar tsaro
  • ECOWAS ta kaddamar da rundunarta mai dakaru 5,000 don yakar ta’addanci
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Suka Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • Pakisatan: An Kubutar Da Mutane 155 Sannan Yan Ta’adda 27 Sun Halaka  A Garkuwan Jirgin Fasinja A Jiya Talata
  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina