Aminiya:
2025-03-15@16:17:27 GMT

Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 

Published: 15th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Saman Najeriya (NAF), sun kashe manyan shugabannin ’yan bindiga guda biyu, Gero (Alhaji) da Alhaji Riga, tare da wasu mayaƙansu sama da 20 a wani hari ta sama da suka kai a Jihar Katsina.

Harin ya faru ne a ranar Laraba, 13 ga watan Maris, a dajin da ke Ƙaramar Hukumar Faskari.

Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin Amurka kan cin zarafin Kiristoci  Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano

Rundunar Operation Fansan Yamma ta NAF ce ta ƙaddamar da harin bayan samun sahihan bayanai kan maɓoyar maharan.

A cewar Mataimakin Kakakin NAF, Kyaftin Kabiru Ali, ya ce dakarun sun lalata sansanin maharan.

“An kashe ƙarin ‘yan ta’adda a tsaunukan da ke kusa, kuma har yanzu ana ci gaba da binciken irin ɓarnar da aka yi musu,” in ji shi.

Gero da Riga sun shahara wajen bai wa ‘yan ta’adda mafaka, waɗanda ke yawan kai matafiya hare-hare a kan titin Funtua zuwa Gusau.

Mutuwarsu ta zama babban ci gaba ga jami’an tsaro da ke aiki tuƙuru don tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Yamma.

“Wannan babban ci gaba ne a yaƙin da muke yi da ɓarayin daji a Katsina da kewaye.

“Sojojin sama tare da haɗin gwiwar dakarun ƙasa za su ci gaba da kai wa maɓoyar ‘yan ta’adda hare-hare har sai an samu cikakken zaman lafiya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Shugabannin Yan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada sanarwan cewa a shirye take da saki fursinonin HKI da Amurka, har ma da gawakin wasu 4, idan HKI ta dawo kan ci gaba da aiwatar da abubuwan da yarjeniyar tsagaita wuta a tsakaninta da HKI.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani Jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Jumma’a. Ya kuma kara da cewa, wasu daga cikin wadanda suke tsakanin kungiyar da HKI ne ya bata wannan shawarar, sannan ya kara da cewa, sai dai wannan matakin yana da sharudda, kuma sune HKI ta amince ta dawo kan tattaunawa marhala ta biyu don aiwatar da yarjeniyar da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.

Taher al-Nounou ya fadawa kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa kan cewa Hamas zata salami Edan Alexander wanda yake dauke da passport na Amurka da kuma wasu 4 wadanda suke dauke da Passport na kasashen biyu wato HKI da kuma Amurka. Amma tare da wannan sharadin.

Sanarwan ta kammala da cewa kungiyar ta fara sabuwar tattaunawa a birnin Doha na kasar Qatar a ranar Talatan da ta gabata sannan tawagar HKI ma tana halattar tattaunawan wand aba kai tsaye ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Dan Majlisa Ya Tallafa Wa Al’ummar Mazabarsa Da Kayan Abinci Na Naira Miliyan 45 A Katsina
  • Sojoji sun ceto mutum 7 daga hannun ’yan bindiga a Filato 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna
  • ’Yan bindiga sun sace gwarzon gasar karatun Alƙur’ani a Katsina
  • ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
  • NAJERIYA A YAU: Ko Sulhu Da ’Yan Ta’adda Zai Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Arewa?
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina