Leadership News Hausa:
2025-03-15@16:15:08 GMT

Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Published: 15th, March 2025 GMT

Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Kungiyar manyan ma’aikatan Jami’oi ta nuna rashin jin dadinta da wasu manufofi na Gwamnatin tarayya musamman ma irin nau’oin harajin da ake cirewa duk wata ya maida albashinsu ya kasance tamkar miyar da babu Gishiri bare Maggi ko kuma Daddawa, shi yasa karin da aka yi na mafi karancin albashi na Naira 70,000 ya zama tamkar tafiyar Kura ne inda take yin Gaba ta kuma koma Baya.

Wannan bayanin ya fito ne bayan da aka kammala taron kwamitin zartarwa na kungiyar manyan ma’aikatan Jami’oi na 50 wanda aka yiu a Jami’ar Gwamnatin tarayya ta Otuoke, Jihar Bayelsa, inda kungiyar ta nuna damuwarta kan manyan lamurra wadanda suke damuwar jin dadin ‘yan kungiyarta,kamar yadda ake samun toge a albashi inda bai kaiwa yadda ake tsammani ko sabawa da ganin hakan, akawus – alawus wadanda aka ki biya, yadda wasu Malamai mata ake neman cin mutuncinsu ta hanyar neman yin fasikanci da su, lalacewar ko rashin abubuwan jin dadin rayuwa a Jami’oi inda wadansu sun gama lalacewa gaba daya.

A takardar jawabin bayan kammala taron wadda take dauke da sa hannun Shugaban kungiyar na kasa Komrade Mohammed Haruna Ibrahim, “mambobin kwamitin zartarwar kungiyar sun nuna rashin jin dadinsu kan abinda suka kira da yawan nau’oin harajin da ake cire masu kowane wata abin ya yi yawa.Kamar yawan albashinka dai dai da yadda za a cire ma haraji mai gwabi (PAYE)Uwa Uba kuma ga karuwr harajin (VAT)wanda babu irin bayanin da za ayi wanda zai gamsar da ita kungiya bare mambobinta.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Matsalar Da Za A Fuskanta Idan Majalisa Ta Tsige Fubara – Wike

Gwamna Fubara da Wike sun samu saɓani tun bayan hawa mulki, lamarin da ya haddasa rikici a siyasar Jihar Ribas, wacce ke da arziƙin man fetur.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Rasha Za Ta Kara Yawan Alkamar Da Take Kai Wa Kasashen Afirka
  • Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike
  •  An Yi Gargadi Akan Rushewar Kungiyar  Agajin Falasdianwa Ta UNRWA
  • Harajin Da Amurka Ke Kakabawa Na Nuna Dabi’arta Ta Kariyar Cinikayya
  • ’Yan sanda sun hallaka hatsabibin ɗan bindiga a Abuja
  • Babu Matsalar Da Za A Fuskanta Idan Majalisa Ta Tsige Fubara – Wike
  • Nazarin CGTN: Manufofin Haraji Na Amurka Sun Rage Kwarin Gwiwa Kan Kasuwar Hannayen Jari Ta Kasar
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina