Leadership News Hausa:
2025-04-14@17:21:08 GMT

Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Published: 15th, March 2025 GMT

Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Kungiyar manyan ma’aikatan Jami’oi ta nuna rashin jin dadinta da wasu manufofi na Gwamnatin tarayya musamman ma irin nau’oin harajin da ake cirewa duk wata ya maida albashinsu ya kasance tamkar miyar da babu Gishiri bare Maggi ko kuma Daddawa, shi yasa karin da aka yi na mafi karancin albashi na Naira 70,000 ya zama tamkar tafiyar Kura ne inda take yin Gaba ta kuma koma Baya.

Wannan bayanin ya fito ne bayan da aka kammala taron kwamitin zartarwa na kungiyar manyan ma’aikatan Jami’oi na 50 wanda aka yiu a Jami’ar Gwamnatin tarayya ta Otuoke, Jihar Bayelsa, inda kungiyar ta nuna damuwarta kan manyan lamurra wadanda suke damuwar jin dadin ‘yan kungiyarta,kamar yadda ake samun toge a albashi inda bai kaiwa yadda ake tsammani ko sabawa da ganin hakan, akawus – alawus wadanda aka ki biya, yadda wasu Malamai mata ake neman cin mutuncinsu ta hanyar neman yin fasikanci da su, lalacewar ko rashin abubuwan jin dadin rayuwa a Jami’oi inda wadansu sun gama lalacewa gaba daya.

A takardar jawabin bayan kammala taron wadda take dauke da sa hannun Shugaban kungiyar na kasa Komrade Mohammed Haruna Ibrahim, “mambobin kwamitin zartarwar kungiyar sun nuna rashin jin dadinsu kan abinda suka kira da yawan nau’oin harajin da ake cire masu kowane wata abin ya yi yawa.Kamar yawan albashinka dai dai da yadda za a cire ma haraji mai gwabi (PAYE)Uwa Uba kuma ga karuwr harajin (VAT)wanda babu irin bayanin da za ayi wanda zai gamsar da ita kungiya bare mambobinta.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

Ilimi Gishirin Rayuwa

Babu shakka ba tun yanzu ba, dan’adam ya dade da fahimtar muhimmancin ilimi ga cigaban rayuwarsa. Walau ilimin addini ko na cigaban rayuwa. Addinin Musulunci ya koyar da mu muhimmancin bai wa ilimi fifiko, kamar yadda aka rawaito a cikin Hadisi. Ma’aikin Allah (SAWA) yana cewa ‘mu nemi ilimi ko da a Birnin Sin ne’. Kuma ya gaya mana cewa, “haddar yaro karami kamar rubutu ne akan dutse…” Kenan, wannan yana karfafa mana gwiwa mu koyawa yaranmu Ilimi tun suna kanana, don za su fi rikewa ya zauna a kwakwalensu. Ilimi tamkar fitila take, yana haskakawa mutum abubuwa na rayuwa, yadda zai koyi zaman duniya da gina wa kansa rayuwa mai inganci. Wannan ilimin kuwa ko da wanda ake koya a wajen aiki ne ko wajen sana’a, ba lallai sai a cikin aji ba. Ana koyon ilimi na aiki da hannu, ko da baki ko a rubuce. Sannan yanzu da zamani ya canza, akwai kafofin sadarwa daban-daban da mutum zai iya samun ilimi ba tare da ya shiga aji ba. Akwai manhajoji irin su YouTube, LinkedIn, Facebook da sauransu da mutum zai iya shiga ya koyi abubuwa da dama na ilimi. Lallai yana da kyau iyaye su rika zaunar da yaran su suna koya musu karatu da ilimin rayuwa, tun daga matakin gida, ko a dauki nauyin mai koya musu, ko kuma a saka su a makaranta. Rashin sa yaro a makaranta na sa ya girma babu wayo, kuma zai rika rayuwar jahilci, da rashin sanin inda yake masa ciwo. Sannan gwamnati ta saukaka hanyoyin samun ilimi, a rika koyarwa da harshen uwa a matakin farko, a samar da ilimi kyau, a rika ba da tallafin karatu ga manya.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To magana ta gaskiya hanyoyin da rashin ilimi ke cutar da al’umma suna da yawa domin shi ilimi jigo ne na rayuwar dan’adam muddun kuwa aka ce babu shi to dole abubuwa da dama ba za su tafi daidai ba, domin shi ilimi dan jagora ne ga duk kanin dan’adam shi ke haskawa mutum hanyar daya kamata ya bi da wacce ya kamata ya kaucewa don matsalolin da rashin ilimi ke haifarwa sun fi gaban kidayawa ko kirdado. To magana ta gaskiya a wannan fannin gwamnati ya kamata ta tashi tsaye wajen inganta fannin ilimin dama samar da shi kyauta ga duk kanin al’ummar kasa, sai kuma iyaye suma su tashi tsaye wajen kulawa da sa ‘ya’yansu a makaranta da kuma kula da zuwan yaran akan lokaci. To magana ta gaskiya kimiyya da fasaha tana bada gagarumar gudunmawa wajen saukaka samun ilimi a wannan zamani da muke ciki shi ya sa za ka ga dukkanin kasashen da suka cigaba ta fannin ilimin kimiyya da fasaha to sun fi samun cigaba a fannin ilimi. To amfanin ilimi ko muhimmancin ilimi ga rayuwar dan’adam ya fi gaban kidayawa ko kirdado domin sai da ilimi ne rayuwar take yin kyau kuma sai da ilimi ne ake samun cigaba a rayuwa. To hakika ya kamata irin wannan iyaye su sake tunani domin fa ilimi shi ne hasken rayuwa wanda duk ya rasa ilimi to ya rasa komai a rayuwarsa don haka ya kamata iyaye su tashi tsaye wajen kulawa da ilimin ‘ya’yansu.

Sunana Fatima Nura Kila A Jihar Jigawa:

Rashin ilimi na haifar da matsaloli musamman a cikin al’umma kamar su sata, fyade, rashin girmama manya duk wadannan rashin ilimi na kawo su. Hanyar daya kamata abi shi ne; Gwamnati ta zage damtse wajen tura yara makarantu da kuma saukaka karatu tun daga matakin firamare, har gaba da sakandare. Ilimin kimiyyya nada matukar amfani ga al’umma ta fuskar tabbatar da sauye-sauye tare da samar da cigaban rayuwa, musamman abin da ya shafi bunkasa tunanin dan’adam wannnan ba karamar taka muhimmiyar rawa yake ba. Ilimi jigo ne sannnan mahadin rayuwa ne, ilimi na da amfani musamman wajen zamantakewa da kuma kasuwancinmu na yau da kullum. Shawarar da zan basu shi ne su bar ‘ya’yansu su je makaranta domin Ilimi shi ne ginshikin rayuwa, mutum mai ilimi ma ya fita daban a cikin al’umma.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Jihar Kano Rano LGA:

Lawan Isma’il

Hanyoyin suna da yawa amma daya daga ciki ita ce; aikata ibada ba daidai ba da sabawa Allah kai tsaye. Samar da ilmi ta internet duk da mafiya yawan wasu mutanen tuni sun yi nisa ta wannan fannin. Wajen kirkirar wasu abubuwan da bamu saba ganinsu ba a yankunanmu. Daya daga cikin amfani Ilmi shi ne; aiki da shi a dukkan al’amuranka. Shawarata a garesu ita ce gaskiya su canja tunani kada iyaye su ga wai yanzu idan ka yi karatu ba a samun aikin yi a’a shi ilmi koda irin ‘yan iskan gari ne za ka ga sun bambanta da wadanda ba su yi ba, a saka yara su yi Ilmi ko wanne iri ne domin a can gaba za a ga amfaninsa. Allah ya sa mudace.

Sunana Aisha T Bello Jihar Kaduna:

Rashin ilimi cuta ce gaskiya, saboda ilimi shi ne kishin zaman duniya, yanzu misali; gida babu miji ya rasu in mata na da ilimi za ta nemi aiki dan ta kula da yaranta. Saboda yanzu duniya da zaran ba maigida ba masu kulawa da marayu Allah ne gatansu. Kimiya da fasaha na taka rawa sosai wajen kawo, cigaba ga al’umma bakidaya. Ga iyayen da basu tura yara makaranta gaskiya babbar cutarwa ce, domin kuwa yanzu duniya ta ci gaba, yanzu idan baka da ilimi kana ji kana gani ka zama dan kallo, don haka iyaye su daure su tura yara makaranta don cigaban al’umma bakidaya. Allah ya amfanar damu baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari