Aminiya:
2025-04-14@16:32:08 GMT

Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC

Published: 15th, March 2025 GMT

Ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya caccaki Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan sukar jam’iyyar APC da kuma Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wata sanarwa da hadiminsa, Seyi Olorunsola, ya fitar, ministan ya zargi El-Rufai da haddasa rikici saboda bai samu muƙamin minista ba.

Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina  Kotun ɗaukaka ƙara ba ta soke naɗin Sanusi II ba — Gwamnatin Kano

Ya ce tsohon gwamnan mutum ne da ƙware wajen haddasa ce-ce-ku-ce da kuma yanke tsauraran hukunci a harkokin siyasa.

Ata ya ce lokacin da El-Rufai yake gwamnan Kaduna, an samu matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, rikicin ƙabilanci da addini.

Ya kuma ce komawar El-Rufai jam’iyyar SDP wata hanya ce da yake ƙoƙarin amfani da ita don a ci gaba da dama da shi a fagen siyasa.

Ministan ya yi watsi da iƙirarin El-Rufai na cewa Tinubu yana haddasa rikici a jam’iyyun adawa, inda ya ce wannan magana ba ta da tushe.

Ya jinjina wa Tinubu bisa jajircewarsa da ƙwarewarsa wajen bunƙasa siyasa, saɓanin El-Rufai da ya ce mutum ne da ke canza jam’iyya akai-akai don son zuciya.

Ata, ya tabbatarwa da ’yan Najeriya cewa APC na ƙoƙarin ci gaba da gina ƙasa, inda ya buƙace su da kada su saurari kalaman El-Rufai.

Ya ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen bunƙasa tattalin arziƙi, bunƙasa ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
  •  A Yau Asabar Ne Ake Bude Tattaunawa A Kasar Oman Akan Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari