’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina
Published: 15th, March 2025 GMT
’Yan bindigar da suka yi garkuwa da wani gwarzon musabaƙar karatun Al-Qur’ani a Jihar Katsina, Abdulsalam Rabi’u Faskari, suna neman naira miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa
Da yake zantawa da manema labarai a ranar Juma’a, Kwamishinan watsa labarai da al’adu na Katsina, Bala Salisu-Zango ya ce Abdulsalam da mahaifinsa da ɗan uwansa da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su, suna nan da ransu a hannun ’yan bindiga, ba a kashe su ba.
Ya ce “Gwamnati ta samu labarin wani saƙon jaje da ake yaɗawa wanda mai ba gwamnan jihar Kebbi shawara kan harkokin watsa labarai ya sa wa hannu, wanda ke nuna cewa ƴanbindiga sun kashe gwarzon musabakar karatun Al-Qur’ani na Najeriya, Abdussalam Rabiu-Faskari.
“Muna godiya da kulawar gwamnatin Kebbi, amma muna bayyana wa duniya cewa Rabiu-Faskari da mahaifinsa da ɗan uwansa suna nan da ransu cikin ƙoshin lafiya a hannun ’yan bindigar.”
Salisu-Zango ya ƙara da cewa ’yan bindigar suna neman kuɗin fansa har naira miliyan 30 ne domin sako mutanen.
Ya ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa domin ceto su, tare da tabbatar da cewa sun koma gida lafiya, yana mai jaddada cewa gwamnatin jihar na ƙoƙari matuƙa domin magance matsalar rashin tsaro a jihar.
Aminiya ta ruwaito cewa, a yammacin ranar Talatar da ta gabata ce ’yan bindigar suka sace mutanen a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Jihar Kebbi.
Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, shi ne ya zo na ɗaya a musabaƙar a ɓangaren maza.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Abdulsalam Rabi u Faskari Jihar Katsina yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka
A baya-bayan nan, jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te, wanda ya kira kansa da “mai rajin neman ‘yancin kan Taiwan”, ya kara ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan ba sa karkashin ikon juna, har ma ya ce wai Taiwan wata kasar demokradiyya ce mai mulkin kanta. Amma duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar da duniya ta amince da ita ba, wato Taiwan ba ta taba zama kasa ba, kuma ba za ta taba zama ba a nan gaba. Sunan yankin Taiwa a MDD shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Manufar Sin daya tak a duniya ra’ayin bai daya ne na al’ummomin duniya, kuma bisa ka’idar ne kasashe 183 suka kulla huldar diflomasiya da Sin.
Ta yaya za a warware batun Taiwan? Tuni dai babban yankin kasar Sin ya tabbatar da cewa, a shirye yake ya yi iyakacin kokari da sahihiyar zuciya domin neman kyakkyawar makomar dinkewar kasar Sin cikin lumana. Amma idan ‘yan aware masu neman “’yancin Taiwan” suka yi tsokana ko tilasta neman ballewa ko ma tabo batu mai tada kura, dole ne zai dauki matakai masu tsauri. Lai Ching-de da mabiyansa da ke wasa da wuta a mashigin tekun Taiwan, za su kone kansu. Sin za ta hada yankunanta, kuma tabbas za su dunkule. Wannan shi ne yanayin tarihi da ba za a iya juyawa ba. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp