HausaTv:
2025-03-17@06:19:04 GMT

Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza

Published: 15th, March 2025 GMT

Rahotannin dake fitowa daga Falasdinu na cewa wani hari da Isra’ila ta kai a arewacin zirin Gaza ya kashe akalla Falasdinawa tara, ciki har da ‘yan jarida uku a cikin gida, in ji ma’aikatan lafiya.

An kai harin ta sama a wata mota a garin Beit Lahiya da ke arewacin zirin yau Asabar.

A cewar likitocin, mutane da dama sun samu munanan raunuka, tare da jikkata a ciki da wajen motar.

“An kai shahidai tara zuwa asibiti, da suka hada da ‘yan jarida da dama da ma’aikata daga kungiyar agaji ta Al-Khair, sakamakon harin da aka kai wa motar da wani jirgi mara matuki a garin Beit Lahia, tare da luguden wuta a yankin,” in ji kakakin hukumar tsaron farar hula Mahmoud Bassal.

Shaidu da sauran ‘yan jarida sun ce mutanen da ke cikin motar na wata kungiyar agaji ve a garin, kuma Sun samu rakiyar ‘yan jarida da masu daukar hoto lokacin da harin ya same su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna

 

Mai Martaba Sarkin Kauru dake Jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci samun hadin kai da aiki tare kana da hakuri da juna tare da ɗaukar banbance banbance dake tsakanin al’umma a matsayin wata baiwa.

Alhaji Zakari Ya’u II yayi wannan horonne lokacin da aka taru a fadarsa dake Kauru domin shan ruwan azumin Ramadan.

Mai martaban ya bayyanawa wadanda suka taru domin wannan aikin lada na shekara shekara cewa, akwai bukatar yafiya da ‘yan uwantaka a wannan lokaci na Ramadan tare da godiya ga Allah da ya sake nuna mana wannan watan mai albarka.

Alhaji Zakaria Ya’u Usman yace akwai bukatar sadaukarwa da mika wuya ga Allah da kankantar da kai tare da fahimtar cewa wannan banbanci da ke tsakanin al’umma wata baiwa ce daga huwallazi tare da kira ga jama’a su nuna godiya ga Allah da wannan baiwar.

Yace Allah baya kuskure, saboda haka mu dauki wannan banbancin dake tsakanin mu a matsayi wata hanya ta aiki tare da nuna karfin mu na zama al’umma daya.

Sarkin Kauru ya godewa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani saboda samarda zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kaduna tare da gamsuwa da yunkurin karamar hukumar Kauru da jami’an tsaron wajen samar da kwanciyar hankali musamman kalubalen tsaron da wasu miyagun mutane suke haddasa wa a yankin.

Ganin yadda bukukuwan sallah ke karatowa, mai martaba ya hori talakawansa su kasance masu riko da kyawawan dabi’u da yafewa juna tare da tunatar da su cewa watan Ramadan ba wai ana magana akan azumi ne kadai ba, akwai bukatar ganin sa a ayukkan mu na yau da kullum.

Haka Kuma, sakataren masarautar Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya nanata kudurin masarautar na samarda zaman lafiya da hadin kai tsakanin al’ummar yankin.

Radio Nijeriya Kaduna ya bada labarin cewa an kammala wannan bikin shan ruwa na masarautar Kauru da gudanar da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaban al’ummar yankin a daidai lokacin da ake shirin bukukuwan sallah.

Yusuf Zubairu Kauru 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen JMI Ta Yi Allawadai Da Kungiyar G7 Wacce Ta Zargin Kasar Da Abubuwa Da Dama
  • Kungiyoyin Falasdinawa Suna  Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Direba ya murƙushe yarinya ta mutu a artabu da jami’an tsaro a Edo
  •  An Yi Gargadi Akan Rushewar Kungiyar  Agajin Falasdianwa Ta UNRWA
  • ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3
  • Somalia: Adadin wadanda suka mutu a harin Al-Shabaab ya haura 10