Gwamnatin Trump na duba yiwuwar sanya takunkumin hana zirga-zirga ga ‘yan kasashen duniya 41 a wani bangare na yaki da kwararar bakin haure da aka kaddamar a farkon wa’adin shugaban na Amurka na biyu.

Wani bayanin cikin gida da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nakalto ya nuna cewa an rarraba wadannan kasashe zuwa rukuni uku.

Rukunin farko na kasashe goma, da suka hada da Afghanistan, Iran, Syria, Cuba da Koriya ta Arewa, za a sanya musu takunkumi baki daya.

A rukuni na biyu, Eritrea, Haiti, Laos, Myanmar, da Sudan ta Kudu za su fuskanci dakatarwar wani bangare da ya shafi bizar masu yawon bude ido da dalibai, da kuma biza na bakin haure, tare da wasu kebantattu.

Rukuni na uku ya hada da kasashe 26 da suka hada da Pakistan, Belarus da Turkmenistan.

Takardar ta bayyana cewa, wadannan kasashe za su fuskanci wani bangare na dakatar da bayar da bizar Amurka idan gwamnatocinsu “ba su dauki matakan da suka dace don magance matsalar ba cikin kwanaki 60.”

A farkon watan Janairu, Trump ya ba da umarnin zartarwa wanda ke bukatar karin binciken tsaro ga duk wani dan kasar waje da ke son shiga Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kudirin Hana INEC Yin Rajista Da Daidaita Lamuran Jam’iyyu Ya Tsallake Karatu Na Biyu

Kudirin ya kuma nemi kafa wata hanyar warware takaddama don magance rikice-rikicen da suka shafi jam’iyyun siyasa, mambobinsu, ‘yan takara masu zaman kansu, da kuma kawance. Bugu da kari, ta tanadi hukunci kan keta haddi da bayar da shawarar gyara ga dokar zabe ta 2022 don cire rajistar jam’iyyun siyasa daga hukumar INEC.

Bayan gabatar da shawarwari, an mika kudirin ga kwamitin majalisa mai kula da harkokin zabe da kwamitin jam’iyyun siyasa domin ci gaba da tattaunawa a kansa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington
  • Trump Ya Dakatar Da Kafar Watsa Labarai Ta VOA
  • Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Hamas ta yi Allah wadai da haramcin da Amurka da EU suka yi wa gidan talabijin na Al-Aqsa
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Kudirin Hana INEC Yin Rajista Da Daidaita Lamuran Jam’iyyu Ya Tsallake Karatu Na Biyu
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda