Gwamnatin Trump na duba yiwuwar sanya takunkumin hana zirga-zirga ga ‘yan kasashen duniya 41 a wani bangare na yaki da kwararar bakin haure da aka kaddamar a farkon wa’adin shugaban na Amurka na biyu.

Wani bayanin cikin gida da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nakalto ya nuna cewa an rarraba wadannan kasashe zuwa rukuni uku.

Rukunin farko na kasashe goma, da suka hada da Afghanistan, Iran, Syria, Cuba da Koriya ta Arewa, za a sanya musu takunkumi baki daya.

A rukuni na biyu, Eritrea, Haiti, Laos, Myanmar, da Sudan ta Kudu za su fuskanci dakatarwar wani bangare da ya shafi bizar masu yawon bude ido da dalibai, da kuma biza na bakin haure, tare da wasu kebantattu.

Rukuni na uku ya hada da kasashe 26 da suka hada da Pakistan, Belarus da Turkmenistan.

Takardar ta bayyana cewa, wadannan kasashe za su fuskanci wani bangare na dakatar da bayar da bizar Amurka idan gwamnatocinsu “ba su dauki matakan da suka dace don magance matsalar ba cikin kwanaki 60.”

A farkon watan Janairu, Trump ya ba da umarnin zartarwa wanda ke bukatar karin binciken tsaro ga duk wani dan kasar waje da ke son shiga Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi

Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran manjo  janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin tunawa da shahid Mahadi Bakiri a garin Tabriz ya bayyana cewa;; Babu yadda za ayi jamhuriyar musulunci ta Iran ta bude tattaunawa da Amurka a karkashin barazana, yana mai kara da cewa; yin gwawarmaya da jajurcewa a gaban masu girman kai da daga hanci, yana daga cikin muhimman koyarwar alkur’ani mai girma da kuma tsarin musulunci.

Manjo janar Salami ya kara da cewa; ta hanyar tsayin daka da dunkulewar al’umma wuri daya, za a kai ga samun nasara.

Haka nan ya kara da cewa; A tsawon shekaru 46 da su ka gabata, al’ummar Iran ta kasance a cikin fadaka wajen fuskantar duk wata barazana.

Bugu da kari kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma ce; Makiyan jamhuriyar musulunci ta Iran masu kekashewar zukata ne, ba su aiki da mandiki, kuma ba su aiki da duk wata halayya ta ‘yan ta ‘yan adamtaka,abu daya tilo da su ka yi imani da shi, shi ne amfani da karfi.

Har ila yau, kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya yi ishara da halayyar HKI da Amurka a yakin Gaza, Lebanon, Syria, Yemen, Iraki da Afghanistan; yana mai kara da cewa; sun tabbatar da cewa, su masu karya alkawali ne, don haka batun tattaunawa da  wadannan makiyan  kuskure ne

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington
  • Trump Ya Dakatar Da Kafar Watsa Labarai Ta VOA
  • Afirka ta Kudu ta yi martani kan korar jakadanta daga Amurka
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Hamas ta yi Allah wadai da haramcin da Amurka da EU suka yi wa gidan talabijin na Al-Aqsa
  • Kudirin Hana INEC Yin Rajista Da Daidaita Lamuran Jam’iyyu Ya Tsallake Karatu Na Biyu
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Kasashen Sin, Rasha Da Iran Sun Yi Kira Da Dakatar Da Matakin Kakaba Takunkumi Na Bangare Guda
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta